"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Saturday, January 31, 2015

HISTORY OF BARIKIN HADEJIA...

HADEJIA A YAU!
BY: S. Ginsau...




Bariki is a Hausa corruption of the English work barrack, The Bariki in Hadejia town is an old Government Reserved Area (G.R.A.) which contains some important colonial structures. It is located in the eastern part of Hadejia town, at the outskirts of the town, about 2km from the Emir's palace. Bariki was built in 1905 mainly to serve as a new base for the British: specifically,as the barracks of the "B" and "C" Company of the imperial army - the Royal West African Frontier Force (RWAFF) - which later invaded and occupied Hadejia in 1906. After the establishment of colonial rule, bariki became the permanent

residence of the divisional officer (D.O) in charge of the Northern Division, His office was also established there. Other British colonial officers such as the divisional medical officer and the works engineer had their residence and offices located there.

The colonial structures at bariki-were initially built with mud blocks, However, after the consolidation
of colonial rule, the mud-buildings were replaced with that of burnt bricks which were manufactured at filin birki, also in Hadejia town, in the early 1930s. After independence in 1960, bariki continued to serve as the residence and office of the (D.O) and other senior government officials. The D.O.'s office also became the first Hadejia Local Government Secretariat, after the 1970 local government reforms.

The colonial structures at bariki-were initially built with mud blocks. However after the consolidation of colonial rule, the mud-buildings were replaced with that of burnt bricks which were manufactured at filin birki, also in Hadejia town, in the early 1930s. After independence in 1960, bariki continued to serve as the residence and office of the (D.O) and other senior government officials. The D.O.'s office also became the first Hadejia Local Government Secretariat, after the 1970 local government reforms. HADEJIA A YAU!

Monday, January 26, 2015

TARIHIN KAFUWAR GARIN MAIRAKUMI.







Hadejia A yau!
posted from Bloggeroid

Saturday, January 10, 2015

TARIHIN RAYUWAR ALH. SHU'AIBU HARUNA.


ALHAJI SHU'AIBU HARUNA HADEJIA.
An haifi Alh. Shu'aibu Haruna a cikin garin Hadejia a shekara ta 1-february 1954, yayi makarantar firamare a Matsaro firamare a shekarar1961-1967, yayi makarantar sakandire ta KEDC dake Kano a shekara ta 1969-1974, sannan yayi N. C. E a ATC/ABU Zaria yayi (Degree) a ABU Zaria a inda ya karanci B. ed a Social Studies a shekara ta 1980-1982, Sannan yayiwa kasa shidima wato (NYSC) a Kwara State a shekarar 1979-1980.

Daganan yayi aikin koyarwa a Auyakayi Auyo LGA, a shekara ta 1974-1975, daganan ya koma Bichi Kano State inda yayi aikin koyarwa a shekara ta 1979-1980, Sannan ya rike mukamin (Principal) a Garo dake Kabo LGA a Kano State, a shekara ta 1982-1986, Alh. Shu'aibu Haruna ya sake rike mukamin (Principal) bayan ya koma Kiru LGA Kano State da aikin koyarwa, a cikin shekarar 1986-1991, Sannan yasake rike matsayin (Principal) a Danbatta LGA Kano State a shekara ta 1991-1992, Sannan ya sake rike da matsayin (Principal) a Kaugama LGA Jigawa State, a shekara ta 1992.

Bayan Alh. Shu'aibu Haruna Hadejia ya gama aikin koyarwarsa lafiya cikin nasara da fatan alkairi da abokan aikinsa suka masa, ya rike matsayin (Director General Ministry of Land & Regional Planing Jigawa State) a shekara ta 1992-1993. Sannan ya sake rike matsayin (Dirctor General Budget & Planing Jigawa State) 1993-1994. 

Alh Shu'aibu Haruna Hadejia, ya rike matsayin (Coucilor Hadejia LG Works & Housing) a shekara ta 1994-1996, Sannan ya Zama  (Member Constitutional Amendement) 1999.
Sannan (Chairman Hadejia World Bank Project) sannan (Asst. Sec. Movement for the creation of Hadejia State). Alh. Shu'aibu Haruna gogegge ne a fagen siyasa ya fara harkar siyasa a 1979. NEPU, PRP, NPN, NCPN, NDP, PDP, ANPP, Yanzu kuma yana APC, Kuma (National Delegate) har zuwa yanzu. ganin irin wannan godewa tasa da hakuri irin nasa yasa mutanen Hadejia
suka Tsayar da shi dan Takarar (National House of Assembly) a 2003, NDP. Mai wakiltar Hadejia Auyo da K/Hausa. Alh. Shu'aibu Haruna babban dan kasuwa ne kuma manomi ne, shine mutum na farko da ya fara kawowa kasar Hadejia cigaban da babu wanda ya kawo kasar Hadejia wato Kamfanin Leda mai suna(NAKOWA PLASTIC
LTD) wanda ya samar aiki ga matasan kasar Hadejia, sanadiyyar daukansu aiki da yayi a Kamfaninsa, wanda yanzu sama da mutum 250 suna aiki a karkashin sa, sannan ya
kawo babban cigaba a Harkokin samar da Wayoyin Hannu wato (Handset).Yana da shagunan da ake siyar da wayoyin hannu da dama a cikin garin Hadejiya, wanda mutane sama da 150, suna aiki a shagonan sa. Sannan (Chairman Nakowa Plastics Ltd) & (Pressident Jigawa Chamber of Commerce Mine & Agriculture.

Alh. Shu'aibu Haruna Hadejiya mutum ne mai hakuri da juriya da sanin yakamata. Mutanan Kasar Hadejiya suna maka fatan alkairi Allah ya daukaka rayuwarka Allah ya taimaki zuri'arka baki dayansu. Allah sauran mutanan kasar Hadejia zasuyi koyi da irin halinka. Allah yasake buda maka kasake kawomana wani cigaban kasar Hadejia wanda mutane zasuna karuwa da ita. Amin.

HADEJIA A YAU!

Saturday, December 20, 2014

ZIYARA DA AMFANINTA.

a.

r">
Ziyara wani Nau'i ne na zumunci wanda mutane suke aiwatar da ita domin sada zumunci ga 'yan'uwa da abokan Arziki. zumunci wata irin halayya ce ta kwarai wacce ke sadar da dangantaka ta nasaba tsakanin ’yan'uwa ko bare. Zumunci ne ke kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali da fahimtar juna tsakanin al’umma.

Ta hanyoyin da mutum zai bi ya inganta zumunci shine, kaiwa ziyara ga 'yan'uwansa kamar kaka, uba kokuma kanin mahaifi ko kanin mahaifiya da sauransu. Ta haka ne mutum zai gane irin yadda Alaqarsa take da 'yan uwansa na nesa ko na kusa. Haka kuma kowa yana da iya kimar zumuncin da zai gudanar a tsakaninsa da wani. Kamar yadda Hausawa suka ce zumunta a kafa take, to wannan gaskiya ne,domin
kuwa daya daga cikin manyan ginshikan zumunta shi ne ziyartar juna. Idan ka kula da zumunci shike sa mutum ya niki gari zuwa gidan abokinka ko wani dan'uwanka, ko bare musamman domin ganin yadda yake. Wannan ziyara kawai, ita ke haddasa kauna da mutunci mai dorewa a tsakanin al’umma.

A shekarun baya kamar shekara kamar goma zuwa sama,saboda muhimmancin ranar Juma'a,iyaye sukan je da 'ya'yansu gidajen 'yan'uwansu da Abokan Arziki domin gaisawa wanda hakan yana nuna ana nusar da yara ne da kaiwa ziyara ga 'yan uwansu. Harma yara suke kiran wannan ziyara da yawon Juma'a. Amma saboda shagaltar da zuciya irin ta shaidan tasa wannan kyakkyawan Aiki na ziyara ya fara ja baya ga yara harma da manyan a wannan zamani,domin shi bubba yana tunanin ai in yaje zai bada kudi, sannan yaro yana tunanin kar yaje ba'a bashi kudi ba.

Wednesday, December 3, 2014

TAKAITACCEN TARIHIN HASHIM UBALE YUSUF..

Hadejia A yau!

An haifi Hashim Ubale Yusufu a Garun Gabas da ke cikin yankin Karamar Hukumar Mallam Madori ta yanzu, A ranar 21 ga Satumba na shekarar 1956. Ya fara karatunsa a makarantar firamare a nan Garun Gabas inda ya fita da kyakkyawan sakamako a matsayin dalibi mafi kwazo da hazaka Daga nan ya wuce zuwa Sakandaren gwamnati dake Birnin Kudu inda ya yi karatu daga 1969 zuwa 1973, lokacin da ya rubuta jarrawar makarantun sakandare ta Afirka ta Yamma wato WASC.

Ya halarci Makarantar Koyon ilimi mai zurfi ta Kano, wato College of Advanced Studies daga 1973 zuwa 1975, inda ya fita da babbar takardar shaida, wato Higher School Certificate. Daga nan kuma ya sami shiga jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria inda ya yi karatun digiri a fannin ilimin harhada magunguna (wato pharmacy) wanda ya gama a shekarar 1981.Bayan ya kammala karatun jami-a, sai sai ya tafi aikin bautar kasa a jihar Imo inda aka tura shi Federal Polytechnic da ke garin Afikpo -Okposi inda ya yi aiki a matsayin mai bayar da magani na wannan makarantar da kuma koyar da darasin chemistry daga 1982 zuwa 1983.Hashim ya fara aiki tun daga matakin karamin ma'aikaci inda a tsawon shekaru ya taka matakai daban daban har zuwa matsayin darakta a hukumar kula da tsaftar abinci da magunguna a Nigeria, da kuma bubban sakatare wato permanent secretary.

Ya fara aiki a shekarar 1974 a matsayinsa na Mataimakin Jami'in gandun daji a karkashin sashen kula da gandun daji na tsohuwar Jihar Kano, sannan daga bisani ya canja aiki zuwa bubban Asibiti na Kano (wanda aka fi sani da asibitin Murtala a yanzu) inda yayi aiki amatsayin jami'i mai bada magani na wucin-gadi a cikin shekarar 1981 da 1982, inda kuma a shekarar 1983 aka daukeshi aiki a karkashin Sashen Kula da ayyukan lafiya kuma aka tura shi Asibitin Murtala da ke Kano a matsayin Jami'in bayar da magani mai daraja ta daya. Daga 1985 zuwa 1987, ya yi aiki a cibiyar sayar da magani ta Lafiya Pharmacy dake garin Hadejia, wadda ta kasance daya daga cikin cibiyoyin sayar da magani da aka bude a wancan lokacin. Bayan daukar lokaci yana aiki karkashin gwamnati,sai ya tsallaka zuwa ma'aikatu masu zaman kansu inda ya yi aiki a kamfanonin sayar da magunguna na NAMCO da kuma ANHEL das u ke cikin binin Kano daga 1987 zuwa 1989. Haka nan ya yi aiki a da hukumar bada tallafin cigaba ta kasar Amurka wato USAID a matsayin jami’in gudanar da ayyuka na kasa karkashin shirin Inganta Lafiyar Iyali (wato Family Health Services).

A shekarar 1989, ya rike mukamin Mai bada shawara a gandun daji na tsohuwar Jihar Kano, sannan daga bisani ya canja aiki zuwa Babban Asibiti na Kano (wanda aka fi sani da asibitin Murtala a yanzu) inda ya yi aiki a matsayin jami'i mai bada magani na wucin-gadi tsakanin 1981 da 1982, inda kuma a shekarar 1983 aka dauke shi aiki karkashin Sashen Kula da ayyukan lafiya kuma aka tura shi Asibitin Murtala da ke Kano a matsayin Jami'in bayar da magani mai daraja ta daya.

Wednesday, October 29, 2014

HADEJIA TOWN WALLS AND GATES.

BY: SULEIMAN GINSAU HADEJIA A YAU! HADEJIA TOWN WALLS AND GATES "Hadejia was a large town with 5 town gates and excellent walls about 30ft (9.14m) high, and 30ft (9.14m) thick " (Captain Philips 1909)

Hadejia Town walls had a long history dating back to the pre-jihad period. The walls were built to provide security to the people, and to serve as fortification against external invasion. Though mostly in ruins now, with a great proportion having completely disappeared, the walls were intact up to the time of the colonial invasion in 1906. Hadejia A yau!

The construction of the walls was done by direct labour using local building materials. Over the years, the walls have been taken subjected to several phases of development. Expansions and reinforcements were made to accommodate a growing population or to enhance security against attack by powerful enemies. The walls were invariably complimented by gates whose history could be linked to that of the walls. The gates provided the only entry points into the town. They were made extremely strong, thus making it very difficult for an enemy force to break into the town through them. Hadejia A yau.

The gates were manned by gate-keepers or porters (sarakunan kofa) appointed by the Emir. These keepers used to close the gates everyday from dusk to dawn, thus controlling the movement of people in and out of the town during these periods. Visitors or strangers were not allowed in unless with the express permission of the Emir. It was reported that one Emir ordered the gates to be left open permanently, confident that no enemy force would dare attack the town.

The first town wall in Hadejia was believed to have been built during the pre-jihad period. Though the exact date of its construction cannot be determined due to lack of proper records, its perimeter is marked by certain well-known local pits: Mai kilabo in the west, Atafi in the south, and Dallah in the East. It was said to be one mile in circumference, and had four gates. The second wall was built by Sarki Sambo in the early years of the Jihad. It was wider than the previous wall, with its perimeter approximately put at 2 miles 170 yards. It had 5 gates. The present wall, which was the third, was also built during Sambo's reign. It was built at a time when Hadejia was at the centre of a bitter rivalry between Sokoto caliphate and Borno Empire. As such it was much stronger and wider than the previous walls. An extension to this wall was later made on the Eastern side during the reign of Sarki Haruna (1865 -1885) encompassing a large space to harbor fugitives from surrounding villages in times of war.


The Habe settlement of Fantai, which hitherto was outside the wall, also became sheltered in the new extension. This brought the wall to its present size of 4miles 135yards, with 5 gates, namely: 

Kofar Gabas (also known as Kofar Gwani) Kofar Arewa KofarYamma Kofar Kyalesu (also Known as Kofar Kogi) Kofar Mandara (also known as Kofar Talata) Apart from the Kofar Mandara gate, which was destroyed by the British in their attempt to gain entry into Hadejia town in 1906, the other gates are still standing in their original positions.


They have, however, undergone several modifications over the years, the latest being in1985 which saw the total re-construction of Kofar Arewa and Kofar Yamma. The Hadejia town gates now stand as historical monuments rather than as security outposts. HADEJIA A YAU BY: SULEIMAN GINSAU -- Sent from A. Sabo note fad. HADEJIA A YAU!

Monday, September 29, 2014

TARIHIN RAYUWAR GALADIMAN KANO A TAKAICE! Alhaji Tijjani Hashim.

Hadejia A yau!< p> An haifi Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim a cikin garin Kano, a shekarar 1932. Mahaifinsa shine Turakin kano Hashim dan sarkin kano Abbas jikan sarkin Kano Ibrahim Dabo. Ya fara karatun Elementary  a garin Bebeji a cikin shekarar 1944. sannan ya shiga makarantar Middile ta Kano inda ya kammala a  shekarar 1951.

A shekarar 1952 Galadiman kano ya fara aiki a  hukumar N. A. (Native Authority) ta Kano a matsayin Malamin Dabbobi, mai kula da tsafta da lafiyar dabbobi. A 1956 aka zabe shi  a matsayin dan majalissa mai wakiltar Sumaila a majalisar dokoki ta Arewa dake kaduna.

A zaman sa a wannan majalisa ne ya rike mukamai da dama ciki har da shugaban hukumar bada kwangila ta Kaduna sannan ya rike shugaban kwamitin tabbatar da jamiyyar NPC ta lashe zabe a lardin Sardauna. Sannan ya rike mukamin Ministan Ayyukan cikin gida na Jihar Arewa. Yayi Kwamishinan lardi mai kula Lardin Kabba wandda yana kan wannan mukamin ne sojoji suka yi juyin mulki.

Bayan ya dawo gida sai  Sarkin Kano Ado Bayero ya nada shi sarautar Dan-isan Kano kuma kansila mai kula da ayyukan gayya da taimakon kai da kai.

A cikin shekarar 1976 ne ya samu karin girma zuwa sarautar Turakin Kano da bashi kulawa da gundumar Kumbotso. sannan A 1980, ya sami canji zuwa kansila marar ofis saboda yawan  harkokinsa na kasuwanci. A shekarar 1989, ya samu karin girma zuwa sarautar Dan-iyan Kano, kuma ya ci gaba rike mukamin kansila marar ofis.

A shekarar 1992, ya samu karin girma a sarauta inda aka nadashi Galadiman Kano kuma shugaban kwamitin kudi na majalisar Sarki. A shekarar 2012 Sarki ya kara masa aikin hakimcin birnin Kano. Wannan aiki ya ke rike dashi har Allah ya masa rasuwa.

Galadiman Kano Tijjani mutum ne mai hakuri da juriya da Alkairi. Kuma yana da daraja a Idanun mtane sakamakon amfani da yayi da damarsa ya kafa mutane a Gwamnati. kuma babu inda zai nemi Alfarma a gwamnati bai samu ba, wannan tasa ake masa Laqabi da GAJERE WAN GWAMNATI.

A ranar28/september/2014, Allah ya yiwa Galadiman kano rasuwa ya rasu ya bar 'ya'ya da Matan Aure da 'yan-uwa da dama. Muna Addu'a Allah ya gafarta masa.

Friday, August 15, 2014

TARIHIN DAN-AMAR DIN HADEJIA M. USMAN GINSAU.

MARIGAYI DAN AMAR ( ALH. MALAM GINSAU) 1917 -1997……………………………..
Marigayi Dan Amar din Hadejia Alhaji Malam Usman Ginsau dan Chiroman Hadejia Ali, dan Sarkin Hadejia Haruna Maikaramba dan Sarki Muhammadu Maishahada ne. Yayi karatun makaranta a garin Hadejia.Yana daga cikin yan makaranta na farko da suko ka bude Clerical College da ke Congo a garin Zaria, kafin ta rikide ta koma ABU Zaria.

Malam ya koma England (UK) domin karin karatu a harkar Community Development. Marigayi Dan Amar ya zama Community Dev. Secretatry na Hadejia N.A. Bayan wannan aiki Marigayi ya kama aikin Gona gadan gadan har zuwa1980.

Ya zama Representative Na Hadejia NA a Old Kano State wanda ya bashi damar shiga Co -operative Society na Nigeria shi da Sarkin Ringim Alh. Sayayadi Mahmudu.Marigayi ya zama 2nd Vice President na Co-operative Society of Nigeria. Yayi Ritaya daga wannan aiki a 1980.

Daga nan Marigayi ya kafa Makarantar Islamiyya da ta Karatun Alkura’ani a Gidansa, shi da kansa yake karantar da mutane, wato manya da yara. Malam yayi ta yin wannan aiki har zuwa 1983 a lokacin da aka nada shi Dan Amar din Hadejia, Hakimin Kafin Hausa.Malam yana daya daga cikin dattijan da suka tsaya wa Kasar Hadejia da addu’a da kuma bada gudummawa wajen duk wani aiki na dattako a Kasar Hadejia. Malam ya rasu ya bar ‘ya ‘ya ashirin da shida.. Daga cikinsu Akwai Dan-Amar din Hadejia na yanzu Alh. Aliyu Usman Ginsau, Hakimin Kafin-hausa, da Baraden Hadejia, Alh. Haruna Usman Ginsau.

Allah ya jikansa ya gafarta masa, ya kara sa albarka a zuriyar da ya bari. Ameen.Posted from WordPress for Android via Hadejia A yau.

Monday, March 17, 2014

TARIHIN JARMAN HADEJIA ALH. ABBA SAMBO (DAGA NA GABA PART FIVE 5)

TAKAITACCE TARIHIN MAIGIRMA JARMAN HADEJIA ALH. ABBA SAMBO!!
Daga Muhammad Yawale.




An haifi Alh. Abba sambo a shekara ta 1943 a cikin garin hadejia, ya fara karatun allo a matakin karatunsa na farko sannan lokacin ya isa shiga makarantar boko. Ya fara da hadejia junior elementary school dake dalla wanda a yanzu ake kira Abdulkadir primary school a shekarar 1953-1957 a garin hadejia. Bayan ya kammala wannan makarantane ya samu shiga middle school a cikin shekarar 1957-1959, daga nan bayan kammala middle school ya koma makarantar horan malamai ta wudil/bichi teachers collage a shekarar 1960-1965.


Bayan kammala wannan karatune ya samu zama headmaster a garin gabas primary school a shekara ta 1966-1971, ya koma karin karatu a advance teachers collage zaria a cikin shekara ta 1971-1974 wanda ya samu certificate in education (NCE). Bayan kamamala (NCE) bai tsaya ba domin samun degree na farko a fannin physical Health Education (PHE) wanda ya kammala a 1975-1978 ABU Zaria. Yayi hidimar kasa (NYSC) a federal advance teachers collage dutsinma katsina state daga 1978-1979.

Wasu ayyuka da yayi:
(1) mataimakin shugaban wasannin motsa jiki gwamnatin tarayya (NSSF) 1985-1989
(2) wakili a hukumar ilimi mai zurfi ta jami'ar Ahmadu
bello dake zaria 1988-1991 
(3) wakilin tantance jarabawar dalibai na kasashen africa 1995. 

(4) shugaban wasannin motsa jiki na makarantun jihar jigawa.


Mukaman da ya rike: (1) shugaban makarantar primary ta garun gabas.(2) jami'i mai kula da shiyar kudu maso yamma wadda take birnin kudu a jihar kano (3) mataimakin shugaban kwalejin makarantar horarda malamai dake garin hadejia (4) mataimakin jami'in ilimi na shiyoyin kananan hukumomin gezawa, da minjibir a jihar kano (5) shugaban makarantar sakandiren jeka ka dawo dake kazaure (6) shugaban kwalejin horar da malamai ta garki. Da sauransu.

Jarman hadejia ya bar aiki ranar 30th ga watan oktoba, 2001 a matakin aiki na 16/17. Bayan rasuwar marigayi jarman Hadejia Alh. Usman sambo na (2) a ranar Asabat 4 ga watan december 2010, maimartaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar maje Con, ya nada ALH. ABBA SAMBO a matsayin JARMAN HADEJIA na (3) a gidan Tafarki Guruza, Jarman Hadejia na biyar (5) a jerin Sarautar Jarma a kasar Hadejia kuma Dan majalisar maimartaba sarki.
HADEJIA A YAU....

Thursday, March 6, 2014

TAURARINMU HADEJIAWA (Part four 4)

DAGA MUHAMMAD IDRIS



Hadejia A yau! 

FARFESA HARUNA WAKILI...............Farfesa Wakili haifaffen kofar fadar Hadejia ne, kuma kamar yadda sunansa ya nuna mahaifinsa shi ne Wakilin kudun Hadejia [Dandalma] wato mai kula da yankin kudancin garin Hadejia.

Farfesa Wakili shi ne Farfesa na biyu a masarautar Hadejia kuma yana daya daga cikin `yan majalissar dattijai na Jami`ar Bayero ta kano kuma babban Alaramma a tsangayar tarihi ta makarantar, harwayau shi ne Mufti akan harkar tarihi a Arewacin kasar nan dominkafafen watsa labarai da dama na ciki da wajen Nijeriya suna dogara da fatawowinsa wajen warware matsalolin tarihi da suka bujuro musu.Baya da harkokinsa na cikin Jami`a Farfesa Haruna Wakili ya rike Daraktan Cibiyar Nazarin Harkokin Siyasa na Jami`ar wato MUMBAIYA dake Gidan Malam Aminu Kano a Unguwar Gwammajar kano.

" Na zaune bai ga gari ba", wanda bai sanJami`a ba, ba zai san gudunmawar Wakiliba domin a shekaru ashirin da biyar da suka gabata duk dan masarautar Hadejia da ya je Bayero ofishin Wakili ne zangonsa, shi kansa ba zai iya kididdige daliban da ya yi wa hanyar karatu a jami`a ba.

"Mai kamar zuwa kan aika" Yana cikin wannan gwagwarmaya Allah [swt] ya yi masa kwamishinan Ilmi na Jihar Jigawa. wannan mukami nasa duk Bahadeje mai hankali ba zai taba mantawa da shi ba domin baya da ci gaba a gyaran makarantu da samar da aiyuka da matasa da ya yi to kuma a lokacinsa babbar bukatarmu da muka dade muna nema ta neman babbar makaranta ta kai ga biya wato muka samu Jami`ar Kafin Hausa kuma aka gina babbar makarantaraiyukan gona ta Hadejia ta bar lungu ta dawo kan hanya.

Farfesa Haruna Wakili cikakken Bahadeje ne ba ya son raini amma yana da kishin al`ummarsa yana son ci gabansu kuma saboda daga darajar wannan masarauta shi rubutunsa ma na digirinsa na biyu akan wannan Masarauta ya yi.a takaice dai rayuwarsa akan bautawa Ilmi take.Hadejawa suna addu`a Allah Ya ba gwanin yafe gwado.



FARFESA HARUNA BIRNIWA............kamar yadda sunansa ya nuna Farfesa Haruna Birniwa haifaffen garin Birniwa ne kuma yana cikin haular masu mulkin garin.Birniwa shi ne farfesa na farko a cikin wannan masarauta kuma farfesa nabiyu a fadin Jihar Jigawa.


Gaba daya rayuwar Birniwa a kan bautawa Ilmi take domin ya kasance daya daga cikin dattawan malamai a Jami`ar Danfodiyo dake Sokoto na shekaru masu yawa kuma ya rike 'provost' a kwalejin Ilmi dake Gumel sannan ya rike kwamishinan Ilmi a wannan Jiha.

Farfesa Birniwa ya bayarda gudunmawa a fagen bayarda ilmi a Jihar nan matuka domin daruruwan mutane sun ci moriyarzamansa a sokoto domin shi 'admission' a wurinsa kamar mutum ya mari budurwa ne don haka za a ya ce wa shi ne ya budewa Hadejawa kofa a sokoto kuma bai bar sokoto ba sai da ya yi dashe.
Lokacin yana 'provost' ma masu rabo sun samu aiki a wurin.Birniwa ba harkar ilmin zamani kadai ya tsaya ba domin fakihi ne a fannin addini kuma fahintarsa da addini ta kara sa kyawawan halayensa sun kara kyautata domin mutum ne mai hakuri da gaskiya da rikon amana da saukin kai.wani abun sha`awa ga halayensa mai unguwarsa a Hadejia ya ce in dai yana gari duk yadda za a je neman ci gaba da shi ake yi. munaaddu`a Allah ya albarkaci bayansa.

Saturday, March 1, 2014

DAGA NA GABA! HADEJIAWA (PART TWO 2)





DAGA HASHIM AMAR...
MUHAMMAD (ABBAS SECRETARY)- Tsohon Sakataren kananan hukumomin Hadejia, Malam Maduri, SuleTankarkar da Guri; tsohon jami'in kula dajin dadin jama'a, a halin yanzu Akawun Majalisar dokoki ta Karamar Hukumar Guri(Clerk).

Wannan bawan Allah ya taka rawar gani wurin samar wa matasa da dama aikin yia lokacin da yake mukamin Sakatare musamman a Hadejia da Guri. Na san mutane da dama da wannan mutum ya samawa aikin yi, cikin su kuwa har da ni kaina.

HAJIYA SABUWA SHEHU- Shohuwar jami'ar ilmi, tsohuwar shugabar makarantar firamare, tsohuwar Sakatariyar ilmi ta Karamar Hukumar Hadejia; daya daga cikin mata 'yan boko na farko a Kasar Hadejia. Wannan baiwarAllah ta taimaka matuka wurin ci gaban ilmin mata a wannan yanki, ita ce ta dauki mafi yawanmata Malaman Makaranta a Hadejia.

Ta wani bangaren 'yar kasuwa ce da ta samar da aikin yi ga matasa ta wannan bangaren, ita ta kafa shagon gudanar da harkokin sarrafa na'ura mai kwakwalwa (Bussiness Centre)na farko a Hadejia. A yanzu haka 'yar kwamitin kwararru ce masu kula da aiyukan Bankin Duniya a Hadejia. Kuma ta na cikin kwamitin kula da Makarantun Firamare da Bankin duniya suka gina a Hadejia.

Wani abin sha'awa ita ta samar da filin ginin daya Makarantar (Shagari Community), ta nemi filin a hannun Karamar Hukumar Hadejia a  madadin LEA, filin yana hannun ta fiye da shekaru goma. Hajiya Sabuwa ta bayar da tsohongidan ta kyauta ga hukumar ilmi (LEA Hadejia) don gina Makaranta, gidan na unguwar Chadi. Allah Ya saka mata da alkhairi, ya yawaita mana irin ta.

Wednesday, February 19, 2014

DAGA NA GABA! HADEJIAWA...(part one 1)


;
*****Ciroman Hadejia Sambo da ne ga Sarkin Hadejia Abdulkadir.Yana daga cikin 'yan boko na farko a Arewa kuma mutum na farko da ya fara zuwa England a Masarautar Hadejia.Ya rike mukamin Dan Majalissar tarayya a zamaninsa kuma shi ne Babban Dan Majalissar Sarki (senior councillor) a wannan masarauta.Idan aka yi Tarihin ci gaban kasar Hadejia ba a sanya Ciroma Sambo ba tamkar an yi tuya ba a sa albasa ba ne.


Ciroma Sambo dan ajinsu Sardauna ne Sir Ahmadu Bello kuma amininsa ne don haka Sardauna ya yi masa tayin mukamin minista amma ya ki saboda ya ce "idan na bar Hadejia to ba za ta ci gaba ba"A takaice dai ciroman Sambo shi ne kashin bayan ci gaban Hadejia, a zamaninsa ne aka yi gagarumin fashin layi wanda ya zama sanadin titunan da muke gani a cikin gari a yau kuma zamaninsa ne aka fara ginin rumfunan kasuwa na bulo.



Zamaninsa aka fara gina asibiti aka ofisosin gudanarwa da muke da su,a dai lokacin aka kawo wayar tangaraho a Hadejia da Malam Madori kuma Saboda hangen nesa da sanin muhinancin ilmi ciroma ya tursasawa jama'a su sa 'ya'yansu makaranta wanda wannan ce ta sa wannan gari ya yi fice a fagen ilmi har a yau.Wato ba za mu iya kididdigewa aiyukan marigayi ciroma sambo ba saboda aiyukansa ya hade masarautar baki daya.



Ciroma sambo shi ne ya koyawa Sarkin Kano Sunusi Turanci saboda zamani. Allah ya albarkanci bayansa domin har yau Hadejia tana cin gajiyar 'ya'yansa da jikokinsa.Marigayi ciroma sambo masanin ilmin addini ne da na zamani, rumfa sha shirgi,mai hannun kyauta,mai dimancaccen tunani, mai kishin Hadejia na farko.An haifi marigayi a 1909 Ya rasu a 1958 wato yana da shekaru arba'in da tara a duniya kenan. Allah ya sa jannatil firdausi ce makomarsa. Amin.

FARFESA MUHAMMAD IBRAHIM YAKASAI 
*************** Farfesa Muhammad Ibrahim Yakasai haifaffan kasar Garin Gabas ne ta karamar Hukumar Malam Madorin Hadejia.Ya samu lakabin Yakasai saboda ya yi karatunsa a gaban yayarsa da ke aure a 
unguwar Yakasai ta kano. Muhammad Ibrahim yana daya daga cikin manyan 'yan boko na wannan Masarauta kuma shi ne Bafulatani na farko da ya samu darajar farfesa a wannan masarauta.Yakasai ya fara malamin makaranta a sakandiren wunti da ke Hadejia na gajeren lokaci sannan ya samu koyarwa a Jami'ar Bayero da ke kano.



Allah ya yi masa nasibi a harkar karatu domin ya kammala karatuttukansa a cikin lokaci takaitacce. Yakasai yana cikin malamai dake taimakawa 'yan wannan masarauta da ma jihar jigawa baki daya wajen samun shiga jami'a.Baya da daukansu kuma yakan dauki al'alar taimakawa wajen warware matsalar da duk wani dalibi ya shiga cikin jami'a.

Yakasai mutum ne mai fara'a,mai saukin kai,mai sanin yakamata,Karatunsa bai sa ya dauki duniya da zafi ba.Muna masa addu'ar zama vice chancellor nan gaba. Hadejia A yau...

Wednesday, February 5, 2014

EMIRE OF HADEJIA ALH.HARUNA ABDULKADIR.

Emir of HADEJIA Alh. Haruna Abdulkadir ruled from 1950, before he was appointed as Chiroma as Distric head of Guri at the age of 12 in 1921, he experienced a poor health for some years, during which the emirate council ischaired by successive Galadimas, the decendent of Jaji on his behalf who takes charge on the administration of HADEJIA town, just like Sarkin Arewa is district head of Birniwa and Sarkin Dawaki administers kirikasamma district.

But while previously, during colonial period, the Tafida administered Kafin Hausa as district head, until more recently when it was given to Chiroma, a son to the Emir. Fallowing Chiroma’s appointment as a chairman of the Kano state local government service commission he was unfortunately obliged to reside at Kano city, leaving Kafin Hausa to be administered by his deputy while he retain the title.

The old emirate council from 1971 – 1975meet more frequently under the chairmanship of the Galadima Yusuf and Adamu, the major responsibilities of that administration rested firmly with Dan’iya,M. abdulkadir Maidugu, himself a grandson a grand of the Emir Abdulkadir and formally Sarkin Auyo and district head of Auyo, he represented HADEJIA inthe Federal House of Assembly. In his return after the abolition of a civilian rule, he was appointed Senior Executive Councillor of the Emirate council in charge of finance, the native administration,works, rural water supplyand community development.

TheTafida alh. Abdulkadir Maigari, another grandson of the emir Abdulkadir was appointed a councillor in charge of Agric and Natural resourses.The Danburan muhammadu Hurdi……………….

.(Culled from “Local Government at Hadejiia 1977” By M. G. Smith)
By Ma'aji I Abubakar.

Monday, January 13, 2014

HAWAN SALLAR GANI (MAULUDI) A HADEJIA 13/01/2014.

HADEJIA A YAU!
Sallar Mauludi ko Gani a Hadejia ya samo asali ne shekara 90 da suka gabata, wato 1910-1925. A lokacin Sarkin Hadejia Abdulkadir aka fara hawan Mauludi ko Gani a Hadejia, kuma ya kirkiro wannan hawa na Gani ne daidai sabuwar shekarar Musulunci, a Inda yake Ganawa da Hakimansa na waje (District heads) domin suyi jawabin Nasarori da Matsalolinda suka samu a kasarsu a shekararda ta gabata.

Saboda bikin yazo daidai da shekarar Mauludin Manzon Allah (s.a.w.) Sarkin Hadejia Abdulkadir sai yakan hau da Yamma tare da Hakimansa kamar yanda abin yake har yanzu. Kuma a ranar da safe akan gudanarda bukukuwa na Nadin sarautar Hakimi idan ta kama. Sarkin Hadejia Abdulkadir yakan yi hawa da hakimansa inda ake zagaya gari kuma a lokacin yakan bi ne ta Unguwanninda suke da Tsangaya domin ya taya Malaman murnar zagayowar ranar haihuwar Manzon Allah (s.a.w.).

Kamar yanda Abin yake har yanzu Sarki zai fito daga fadarsa da yamma, zai bi ta Tudun mabudi ta Kasuwar kuda sannan yabi ta Kasgayama zuwa Kwarin madaki, sai ya fito ta bayi zuwa Magama hudu zuwa Unguwar Dukawa zuwa Hudu, sannan zai wuce ta Tagurza zuwa Majema zuwa bakin kasuwa, sannan sai ya biyo ta Makwallah zuwa Baderi zuwa Kofar Liman. Sannan ya koma fadarsa. Hadejia A yau.

Monday, December 30, 2013

TARIHIN KAFUWAR HADEJIA A TAKAICE..

HADEJIA-TARIHIN KAFUWARTA Ya farune daga wani maharbi mai suna Hade, a yawon farauta da yakeyi ne wata rana yana tafe da karyar sa sai tayi nisan kiwo ko da tazo sai yaga duk jikinta da ruwa, sai yayi mamakin hakan har ma sai yabi sawunta. Koda yaje sai yaga kogi kuma ga tsuntsaye suna shawagi a gurin. Sai ya yanke shawarar zama a wannan gurin, kuma hakan yayi. Anan ya zauna yayi bukkarsa yake harbe harben Namun daji kuma yayi suw, wato kamun kifi. In ya kashe namun daji sai yaje ya sayar da fatun. Harma ya dauko Matarsa wato Jia ya dawo da ita wannan gurin. Kuma mutane sai suke zuwa sayen fatu da nama a wajensa. Duk wanda yazo gurin sai yayi sha'awar zama a gun, haka nan gari ya fara bunkasa wasu maharba, wasu masinta, wasu kuma mafarauta. Sai gari ya kafu kowa yazo wucewa sai ya yada zango a garin. To kasancewar gari sai da shugabanci ne yasa shi Hade ya zama shugaban garin, duk wanda zaije sayen fatu ko nama sai yace na tafi garin Haden jia. Wato ana masa lakabi da sunan matarsa. sakamakon takaita kalma irin ta Bahaushe sai aka dunkule sunan ake cewa Hadejia. Kuma bayan zamanin wannan mutumin Hadejia taci gaba da zama gari kuma tare da shugabanci wato mulkin Habawa. Hadejia A yau! Kuma a lokacin akwai kananan Garuruwa masu cin gashin kansu kamar Rinde, yayari, wunti, Anku da dai sauransu. Wadanda suma suna da nasu sarakunan a wannan Lokacin. Amma yanzu duk unguwanni ne a cikin garin Hadejia. Kuma Hadejia sunyi sarakunan Habe guda talatin da biyu(32) amma sunan mutum uku ake dasu wadanda sukayi mulki kafin zuwan Fulani. 1, BAUDE 2, MUSA 3, ABUBAKAR. Kuma a lokacin Abubakar fulani sukazo kasar Hadejia, kuma shine ya basu masauki a Hadejia Lokacin Hadejia tana karkashin Mulkin Habawa ne, kuma ya nada Umaru a matsayin Sarkin fulanin Hadejia. Wato kafin Jihadin Shehu usman dan fodiyo. Kuma har yanzu fulanin sune suke sarautar Kasar Hadejia. Hadejia A yau..

Sunday, December 1, 2013

TARIHIN GIZMAWA (NGZIM) DA AL'ADUNSU.

By Comrade Garba Muhd. Hadejia.

GIZMAWA KO NGZIM. Wani sashe ne na Kanuri (Bare-bari) wadanda sukazo daga Borno. Kanuri dai sun kasu gida uku (3), akwai:
Mangawa
Gizmawa
da Larawa.

Mangawa Akasarinsu anfi samunsu a kasar Birniwa da Kirikasamma.

Gizmawa ana samunsu mafi yawa a kasar Guri. A garuruwa irin su Guri, Arin, Dagana, Joriyo, Adiyani, Zugo, Wacakal, Garmaguwa, Garbagal, Margadu,Tukuikui, Dole, Abir da sauransu.

Larawa kuma sunfi yawa a tsakanin Badar, Jigawa, da Bauchi ta kasar Guri. Ana samunsu a Garuruwa irin su: Takazza, Damegi, Gaduwa, Musari da sauransu.

Banbancin da ke tsakanin Gizmawa da Mangawa da Larawa bash da yawa. Kamar banbancin Hausar kano ne da ta katsina ko Hausar sokoto da ta Hadejia. Amma ko wanne yana fahimtar kowane tsakaninsu, wato banbancin a karin harshe ne, kuma a haka suke gane wannan kabilar Ba gizme ne ko Bamange.

Su kuma Kanurin Kadira sun sha bam ban da Gizmawa Larawa da Mangawa. Domin su suna Barbarci ne irin na Borno. Saboda haka ko tsarin zamantakewarsu da sarautarsu ya sha banban.

A bangaren al'adu da zamantakewa basu da bambanci da juna. (Gizmawa Mangawa da Larawa). Tsarin Addinin Musulunci da cudanya da Hausawa ta sa Al'adu da dama na Gizmawa sunyi watsi dasu. Kamar kidan Bango; Rawar Dimas; Rawar biki da al'adun Aurensu duka yanzu ba sosai ake yinsu ba da yawa Hausa ta kwace su.

Wani zaiyi tambaya me yasa aka samu kashe kashen kanuri har gida uku? Dalili shine, zamantakewa da ta bambanta aka samu watsuwarsu a kasar Hausa.

Rabewar Daular Kanem-Borno da Zuwan Rabeh ne yasa wasu daga cikinsu suka tsinci kansu a Daular Usmaniyya, wadda take cike da Hausa Fulani. Kanurinda suke yankin Masarautar Hadejia Musamman ma kasar Guri, sun gauraya da Badawa da fulani da Auyakawa. Hakan tasa karin sautin muryarsu ya sha bamban da kanurin Borno da Yobe. Sannan Al'adunsu sun jirwaye da na Hausawa.

Sannan tsarin Sarautarsu yasa dole suke Amfani da Bulama Maimakon Mai ko Lawan. Amma kuma har yanzu a garin Kadira zaka Iske Kanuri ne suke rike da sarautar garin tare da Badawa da kuma Hausa-fulani kadan.

Sannan ba'a iya bambance Bagizme ko Bamange ko Balare a fuska, domin daga cikinsu zaka iya samun Abubuwa kamar haka:-
*Zube (zane)
*Sutura
*Karin harshe
*Al'adun Aure
*Sana'a
*Tsarin Auratayya
*Addini
*Zamantakewa
*Sunaye
*Son girma
*Kishin yare
*Gardama
*Bajinta
*Ki fadi.

Zane a fuska ya danganta da tsarin iyayen mutum, wadansu iyayen suna da Sha'awar a yiwa 'ya'yansu zube, wasu ko basu da ra'ayin hakan. Saboda haka a cikinsu ana samun mai zube ana samun marar zube.

Barebari ______ Borno

Bamange______ Kirikasamma
Birniwa.

Bagizme________ Guri, Adiyani, Zugo, Gabargal.da sauransu.

Balare__________ Gaduwa, Musari, Takazza, Margadu.da sauransu.

Hadejia A yau.

Sunday, November 24, 2013

TARIHIN HARUNA UJI DA WAKOKINSA. KASHI NA BIYU (2).

Hadejia A yau!



Littafin Muhd. Aji Hadejia.

A kashi na farko kunji cewa Alh. Haruna Uji ya ci gaba da kidan Gurmi gadan gadan.

A lokacin Gwamnan Kano Abdu Bako, sai yaji labarin Haruna Uji, sai yasa aka nemoshi domin yayi masa waka akan wayar da kan Al'umma akan Noma. Saboda haka Gwamna Abdu Bako sai ya hadawa Haruna Uji kayan wasa, kamar Amsa Kuwwa (Loud speaker) da Abin Magana wato (Microphone) da Injin wuta, wato Generator.
Wannan shine lokaci na farko da Haruna Uji ya fara waka da kayan wasa na zamani, kuma ya kama yin waka gadan gadan a matsayin sana'a.

Wakar da yayi a lokacin Itace wakar Noma. Anyi wakar ne da nufin wayar da kan Talakawa su koma Aikin gona.

3.0. WAKOKIN HARUNA UJI NA FARKO.

Alh. Haruna Uji yayi wakoki masu tarin yawa, kuma a cikin Jerin wakokinsa ga wasu daga cikin wakokin da ya fara yi.

*Wakar Naira da kwabo sabon kudi.

*Wakar Gudaliya.

*Wakar Shamuwa.

*Wakar Noma.

*Wakar Bakar Rama.
Wadannan sune kusan Shahararrun wakokin da ya fara yi.

3.1. Ajin Haruna Uji a tsakanin Mawakan baka.

A cikin wani Littafi da Ibrahim Yaro Yahya da Abba Rufa'i suka tsara, Mamuda Aminu ya kawo rabe-raben Mawakan baka zuwa rukunai kamar haka:
*Mawakan Sarakuna
*Mawakan 'yan mata
*Mawakan Jama'a
*Mawakan Mafarauta. Da sauransu.

Ya kawo misalin Mawakan Jama'a shine wanda zai yiwa Sarakuna da 'yan kasuwa da 'yan mata da Masu kudi da talakawa waka. Misali Mamman shata da Haruna Uji da sauransu.

Hakan ta nuna cewa Haruna Uji ya kasance a cikin Mawakan Jama'a, domin ya tabo duk abinda aka zayyana a sama. Wato yakan yiwa kowa waka.

3.1.1 Dangantakar Haruna Uji da Mawakan Baka.

Alh. Haruna Uji yana da kyakkyawar dangantaka da sauran 'yan uwansa mawakan baka, yana girmamasu shima suna girmama shi, sannan ya hori wasu suma sun zama shahararrun mawaka a kasar Hausa. Yayiwa wasu waka kuma shima wasu sunyi masa. A cikin mawakan da suka masa waka har da Alh. Mamman shata, kuma shima Haruna Uji yayi wa Alh. Garba sufa wakar Ta'aziyya bayan ya mutu.

3.1.2 Jerin wasu daga wakokin Haruna Uji.

Bayan rukunin wakokinsa na farko, ga wasu daga cikin wakokin da yayi.

*Wakar Dankabo
*Wakar Alh. Sani Likori
*Wakar Direban Chiyaman
*Wakar (Air vice marshal) Ibrahim Alpha
*Wakar (kwamishinan 'yan sanda) Daudu Gwalalo
*Wakar Haruna karamba
*Wakar Adamu Hassan Abunabo
*Wakar Ahmed Aruwa
*Wakar Asabe Madara
*Wakar Amadu koloji makwallah
*Wakar Bako Inusa kano
*Wakar Balaraba
*Wakar Jimmai Aljummah
*Wakar Birgediya Abdullahi shalin.
*Wakar Dankamasho
*Wakar Fulanin Jebbi fulato
*Wakar Idiyo Mai kayan Babur
*Wakar Kainuwa.

SAURAN WAKOKIN KU DUBA LITTAFIN.

Ka duba kashi na uku (3)

Thursday, November 21, 2013

TARIHIN HARUNA UJI. DA WAKOKINSA. KASHI NA DAYA (1).

Alh. Haruna Uji Hadejia.

Hadejia A yau! An haifi Alh. Haruna Uji A Unguwar Gandun sarki dake cikin garin Hadejia, a shekarar (1946). Sunan Mahaifinsa Mallam Ibrahim, Malami ne kuma shine Limamin Gandun sarki. Sunan Mahaifiyarsa Zainabu itama mutumiyar Unguwar ce. Anan ya tashi yayi wayo. Yana kimanin shekara shida mahaifinsa ya sakashi a makarantar Allo dake kofar gidansu, a gun wani Malami da ake kira Mallam Alhaji.

Haruna Uji ya shafe wajen shekaru uku yana wannan Makaranta a Gandun sarki, daga nan suka tashi da malaminsa zuwa garin Birniwa wanda take gabas da Hadejia, mai nisan kilo mita 45. Sun kwashe shekaru kamar biyu suna karatu da sauran Almajirai, anan Uji ya samu karatu mai dama.

Bayan nan suka bar Birniwa suka dawo Hadejia suka ci gaba da karatu a Gandun sarki. Wannan yasa ya samu karatu mai dama fiye da sauran yara musamman wadanda suka zauna a gida basu fita wani guri neman Ilmi ba. A wannan lokaci Mallam Alhaji yakan sa Uji ya kula da yara tare da koya musu karatu. Haruna Uji ya bar makarantar Allo yana dan shekara goma sha biyu, bayan ya samu karatu mai dama.
Hadejia A yau!

1.1, ASALIN INKIYAR HARUNA UJI..
Sunansa na yanka Haruna, yaci sunan wan Mahaifinsa, wato Mallam Haruna. Mallam Haruna mai sunan Uji yana da mata mai suna IYA KURA, Lokacin Uji yana karami matan kanin Babansa suna masa wasa suna ce masa Mijin Iya Kura, Mijin Iya Kura' A wannan Lokacin yara kannensa basu da baki, sai suke ce masa, Ujin Iya Kura. Maimakon Mijin Iya Kura. Wannan shine Asalin inda Haruna Uji ya samo Inkiyar Uji. Tun ana danganta sunan da Iya Kura har aka daina ake cewa Uji.

1.11, SIFFAR HARUNA UJI.
Haruna Uji baki ne, mai matsakaicin tsawo, yana da jiki matsakaici, ga farin hakora da bakin gashi, yana yawan barin gashin baki, ga magana (Idanu) haka kuma, ma'abocin barin suma ne, yana da Murya mai zaki da kauri kadan, kuma Gwanin Ado ne, da manyan kaya na sarauta. Kuma yakan saka 'yar shara, musamman lokacin zafi.

Alh. Haruna Uji mutum nd mai fara'a da kyauta, domin abin hannunsa bai rufe masa ido ba. Yana da raha sannan kuma bashi da wata nakasa a fili.

2.0, SANA'OIN HARUNA UJI..

2.1, Farauta da Noma.
Bayan Haruna Uji ya bar makarantar Allo, ya fara zuwa Daji da nufin farauta. Wadda itace sana'arsa ta farko, wanda ya fara, kuma ta sanyashi jarunta inda ya zama bashi da tsoro. Kuma a nan ne ya samu tambaya wato lakani na tsare kai.

Bayan farauta Haruna Uji Manomi ne, ya fara aikin gona ne da taya mahaifinsa, domin neman tabariki, wannan tasa yasan harkar noma wanda har yake noma gonar kansa.

2.2, Sana'ar Tukin Mota (Direba)
Alh. Haruna Uji yayi Sana'ar Tukin mota, wanda ya fara da Yaron mota a gun Mai gidansa wanda ake kira da suna Jibrin Dan Amingo. Jibrin Dan Amingo dan Asalin Danbatta ne ta Jihar Kano. Haruna Uji ya shafe shekaru da dama yana sana'ar yaron mota. Tukin mota ne sana'arsa ta farko da ta fara fitar dashi wani gari da nufin zama. Suna aiki ne tsakanin Kano da Hadejia.

Kuma a wannan lokacin suna zaune ne a garin kano a Tudun wada. Amma duk abinda ya taso a gida dashi akeyi, musamman aikin gona da bukukuwa da sauransu.

2.3, Sana'ar Waka.
Haruna Uji bai gaji waka ba, domin Mahaifinsa Malami ne, kuma ko a wakarsa ta Gurmi ba Haramun ba yana cewa:-
"Ni Haruna dan Mallam nake, Waka ta ba ta gado bace"

Saboda haka tun farko Haruna Uji ya riki waka ne a matsayin nishadi, domin ba wanda ya koya masa waka a matsayin Sana'a.

Haruna Uji ya fara ganin Gurmi ne a gun wani ma'aikacin titi wanda sukayi aiki a hanyar Mallam madori zuwa Gumel, wanda ake kira Dan-mato, a gun Dan-mato Uji ya fara ganin Gurmi da kidansa, shi Dan-mato yana kada Gurmi ne a yayinda suka samu hutun aiki. Yana kadawa yana waka, lokacin Uji yana Matashi, duk lokacinda sukaje kallon aiki sai su tsaya suna ganin kidan Gurmin Dan-mato, wannan tasa kidan Gurmi ya shiga ran Haruna Uji, idan ya dawo gida sai yakan nemi gwangwani da tsirkiya ya hada Gurmi yana kadawa. Har Dan-mato suka hada aikin hanya bai koyawa Uji Gurmi ba, sai dai Uji yana zuwa yana ganin yanda yake kadawa. Wannan tasa Uji ya dinga kwaikoyon Dan-mato tun bai iya ba har ya koya.

Wannan yasa idan yana gurmi yara sukan tsaya suna ji da kallonsa, Wannan shine Asalin koyon Gurmin Haruna Uji. Daga nan sai ya fara tunanin ya samu sanda, da lilo da butar Duma da fatar Damo da Zobe domin ya hada bubban Gurmi.

Farkon lokacinda ya fara Gurmi idan an bashi abu baya karba, don yanayi ne saboda Nishadi. Kuma sau da yawa idan ya fito hira ko ana wani biki na samari da 'yan mata, yakan kada Gurminsa yana waka, samari da 'yan mata suna kallo.

A wancan lokacin yana Gurmi yana aikin Mota, wannan yasa ya fara Gurmi a garuruwa daban daban na Arewacin Nigeria.

Daga nan Uji ya bar tukin mota ya koma kidan Gurmi Kuma ya nemi mataimaka don sunayi su biyu.

Karashe a kashi na 2.
Littafin Muhd. Aji Hadejia

Tuesday, November 19, 2013

ZAMANTAKEWA TSAKANIN MANOMA DA MAKIYAYA A KUDANCIN GURI. (KASHI NA 2)



BY COMRADE GARBA MUHD HADEJIA


A lokacin da makiyaya su ka fara yin ta'adi a gonakin mazauna yankin ba a gayyaci kowace hukuma a cikin al'amuran ba, ganin cewar matsalar karama ce a wancan lokacin. Kuma su manoman basu san hakikanin irin fulanin da suke yin wannan ta'adin ba. Har su kan yi tunananin cewar wai shin fullo-Hadejia ne ko Zamfarawa?


Faruwar hakan ta ja hankalin shugabannin mazauna yankin (manoma) wadanda suka hada da Dagatai,Bulamai, Lawanai (Bade), Mai (Gizimawa) don tattauna matsalar da shugabannin Fulani irinsu Lamidai da Hardawa. Irin wannan tattaunawa ta yi ta faruwa har hukuma ta shigo cikin sabgar don rushe dukkan wani yunkuri na barkewar rikici. Saboda abin ya na faruwa duk shekara musamman ma da kaka. Duk da shigowar hukuma cikin lamarin, bai hana daukar fansa daga manoman ba, saboda kai su bango da makiyayan suka yi na cinye musu amfanin Gonakinsu.


A duk shekara a kan asarar rayuwa daga kowane bangare. Duk da kasancewar jami'an tsaro kala-kala; yan sanda, mobile police, wani lokaci har da sojoji don sasanta tsakanin manoma da makiyaya. Suma jami'an tsaron daga bangarensu sun rasa da yawa daga cikin mutanensu. Wasu an harbe su da kibiya, wasu an sassarasu da arda sun mutu wasu an lagarta su, saboda hukuma bata basu damar harbi ba.


A kwai shekarar da har jirgi mai saukar ungulu (Helcopter) aka kai yankin don shiga surkukin dajin da ke wannan yankin. Daga cikin matsalolin da jami'an tsaro su ke samu daga wannan yankin, shine rashin basu umarnin daukar mataki na kare kansu daga dukkanin wanda zai yi yunkurin harbinsu ko sararsu. Haka tasa suke janye jikinsu daga shiga cikin rigimar gadangadan. Daga bangaren gwamnatocin siyaya an samu da yawa da suka taka rawa don ganin an shawo kan matsalar amma idan shekara ta zagayo sai an yi.Haka kowace gwamnati take yi.


A lokuta da dama akan kafa kwamatoci na musamman wanda zaiyi bincike akan matsalar, amma daga karshe sai a kasa cimma komai. Su kan nemi zama da kungiyar manoma da makiyaya da shugabannin kowane bangare don kowa ya jawa mutanensa kunne amma daga karshe sai abin ya bi iska. A wasu lokutan korafe-korafe su kanyi yawa daga bangarorin biyu na zargar junansu da laifin tayarda rigimar. Makiyaya su kan ce laifin manoma ne da suke noma makiyayar dabbobi da burtalai, su kuma manoma su ce laifin makiyaya ne da baza su yi hakurin barinsu su tare amfanin gonarsu ba.

Haka dai ake ta maganganu a kai. Daga lokacin da gwamnati mai mulki a yanzu ta hau. Ta yi kokarin lallai kowane makiyayi ya tsaya a makiyayarsa. Sannan ta tabbatar da kowane burtali da makiyayar dabbobi ba a nomashi ba. Sai dai wani abin mamaki har yanzu abin bai chanja ba, domin wannan rigimar bata mutu ba. Ko shekarar da ta wuce ma an sami rikici a wasu garuruwa irin su Gagiya da Garin Mallam. wadanda su ke kudancin Guri. Ko a wannan lokaci da ka ke karanta wannan rubutun ma, an sami wadansu daga cikin makiyaya suna shiga gonakin manoma suna cinye musu Amfanin gona. Wannan matsalar ta kawo ci baya gagarumi a kudancin Guri. Domin manoma da yawa sun hakura da noman shinkafa, Alkama, Wake da kankana. Abin da ya rage kawai sai gero da dawa, wanda a yanzu a kansu ake yin wannan rigimar domin shi din ma yana neman fin karfinsu.

Babban dalilin da ya sa manoman su ka hakuri da noma wadansu daga cikin amfanin gonar shine. Yawan zubda jinin al'umma da ake yi sakamakon kare dukiyoyinsu. Saboda wasu lokutan har garuruwansu (manoman) ake binsu don a halaka su. Wata shekara akwai garin da aka kona kurmus; tare da abincinsu, da dabbobinsu da dattijai da kananan yara wadanda ba za su iya guduba. Daga karshe, ina kira ga duk wanda ke ziyartar wannan dandali mai albarka, kuma ya kasance mai iko, da ya isar da wannan sakon ga hukumomin da abin ya shafa su duba al'amarin wadannan bayin Allah don kawo masu karshen wannan matsalar.


Sannan 'Yan majalissu na tarayya da na jiha da su kalli wannan abin ta hanyar janyo hankalin gwamnatin tarayya da kungiyoyi masu zaman kansu da su tallafa wajen warware wannan matsalar. Abin da gwamnati ya kamata ta lura da shi, shine wannan matsala ce ta cikin gida tsakanin manoma da makiyaya. Kuma suma wadannan makiyaya (fulani) 'yan uwanmu ne musulmi, sannan mun zo daga bangare daya, kuma tare muke zaune, kasuwa da ya muke ci da su ga auratayya ta hada mu.

Saboda haka ba sai da bakin bindiga za a sasanta ba, a'a akan tabarma za a zauna tare da kwararru a fannin warware rikici wadanda suka karanta (conflicts Resolution) da malaman addini da sauran masu fada a ji a cikin al'umma don a tabbatar da adalci tsakanin manoma da makiyaya. HADEJIA A YAU.

Sunday, November 17, 2013

ZAMANTAKEWA TSAKANIN MANOMA DA MAKIYAYA A KUDANCIN GURI...(1)

Hadejia A yau!
Daga Garba Muhammad Hadejia....
CIWON CIKIN BAREWA A DAJI.

Zamantakewa wata aba ce wadda ta ke kasancewa tsakanin kowane jinsi, na mutane, aljannu, dabbobi da tsuntsaye da sauran halittu. kowane jinsi daga cikin halittu yana da irin kalubalensa na neman cika jakar ciki da sauran bukatu wadanda dole sai an cimma su za a samu dorewar rayuwa, sannan rayuwa ta bada zaman lafiya.

Idan ko ya kasance wani ko wasu daga cikin wannan jinsi zasu fifita bukatunsu fiye da na 'yan uwansu, to za a iya samun barkewar rashin jituwa, wanda shine zai yi sanadin barkewar rashin zaman lafiya a tsakanin wannan jinsin.

Dan Adam, wanda ya kasance mafi hikima a cikin sauran halittu,saboda wadansu ni'imomi da ubangiji ya yi musu. Shi kadai ne ya ke da tunanin ya noma abin da zai ci, don samun dorewar rayuwa, da nisanta daga galabaita da zai yi a yayin da ya nemi abinci ya rasa a muhallinsa. Daga cikin
abin da ya noma har da tunanin tanaji don gaba yayi amfani da shi.

Kasancewarsa mai hikima (Dan Adam) Allah ya bashi ikon sarrafa wasu daga cikin dabbobin gida, kamar su shanu, awakai, tumakai,rakuma da sauransu.

Daga cikinsu (Yan Adam) akwai wadanda suka zabi kasancewa da dabbobi a matsayin dukiya. Wanda hakan ya sa dole su ka kebe kasu daga cikin jama'a don su samu damar kula da dabbobinsu ta hanyar ciyar da su da shayar da su daga ciyayi da ganyayyaki. Hakan yasa wasu daga cikinsu ko noma ba sa samun damar yi, sai dai su sayi abinci daga manoma ko a kasuwa daga kudaden da suka samu a yayin da suka sayar da dabba ko nononta.

Wani lokacin sukan yi bulaguro daga wani yanki zuwa wani yanki don samarwa dabbobinsu abinci, musamman a lokacin rani ko damana su kan tashi daga yankin da bai da ni'ima zuwa yankin da ya ke da ni'ima.

Haka ta sa ake ganinsu a mutanen da ba su da takamaiman gari, kasa ko nashiya.


Kudancin Guri ya kasance mafi ni'ima idan aka hada shi da sauran yankuna na masarautar Hadejia. Domin albarkatu na daji, fadamu, gurin kiwo, kifi, tsuntsaye, da sauran albarkatun noma. Haka shine ya sa makiyaya suke da yawa a kudancin Guri.

Idan aka ce kudancin Guri ana nufin Gundumar Kadira ko muce (Kadira Distric) sun hada da manyan garu-ruwa irinsu Kadira, Abunabo, Musari, Gaduwa da Galdimari, Garin Mallam, Gagiya,Garmaguwa daSauransu.

Wannan yanki ya hada yaruka (kabilu) masu yawa sabanin sauran yankuna na Masarautar Hadejia. A wannan yanki za ka samu Mangawa, Gizimawa, Badawa, Fulani, Larawa, sai kuma Hausawa Auyakawa wadanda ba su da yawa.
Daga shekarar 1980 ne aka fara samun shigowar makiyaya (Fulani) a wannan yankin.

Fulanin da suka fara zuwa sun kasu kashi hudu, akwai:
Aborawa, Zamfarawa, Udawa, Fullo-Hadejia da Wuddurawa.

Wadanda su ka fara zuwa sune Aborawa. A wancan lokacin sukan zo a lokacin da ruwa ya gama cin dajin ciyawa ta fito sannan su yi kiwo. A wannan lokacin ya kasance a kwai wani ruwa da ake kiransa da suna Ruwan Dukuku; shi wannan ruwa idan ya zo ya kan mamaye dajin gaba daya, ya zamanto babu makiyaya. Hakan yake sa dole makiyayan su yi hijira zuwa kasar Yobe (Bade) don yin kiwo kafin ruwan ya janye su dawo.

Haka aka yi ta tafiya har Udawa su ka fara zuwa don yin kiwonsu a wannan daji kamar yadda Aborawa su ke yi. Su ko mazauna yankin su kanyi nomansu iri-iri, tare da sana'a ta kamun kifi.
Daga cikin Aborawa da Udawa aka samu Fulani mazauna wanda ake kira da Fullo-Hadejia. Sun kafa garuruwa irinsu; Safami, Maidashi, Matarar kano, Dolewa,Askandu da sauransu. Su kan zauna tare da dabbobinsu a rigagensu kuma su kan yi noma a guraren. A yayin da ruwan dukuku ya daina cin Dajin.

Daga nan sai zuwan zamfarawa.
Zamfarawa sun shigo kudancin Guri ne sakamakon fitintinu da ke yawan afkuwa a yankunansu na Zamfara.
Sakamakon haka ne ya sa su ka yi Hijira daga can suka zo kudancin Guri. Sun kasance ba mazauna guri kawai ba, sukan yawata zuwa sauran yankuna na Guri har sukan zuwa makwabta irinsu madaci, marma da sauran guraren da ake noman shinkafa don yin kiwo.

Haka zamantakewa ta ci gaba da kasancewa tsakanin wadannan al'ummah har zuwan Wuddurawa wadanda sukazo daga kasar Katagum da sauran yankunan jihar Bauchi. Domin kudancin Guri ya yi iyaka da Bauchi.

Zumunci tsakanin mazauna yankin da makiyaya (Fulani) ya ci gaba da kulluwa, sakamakon cudanya ta cinikayya da sauran al'amura na yau da kullum ya sa har auratayya ta fara kulluwa a tsakaninsu. Wannan ya sa duk auran da za a yi a Rigar fulani sai ka ga daya daga cikin mazauna yankin ya halarta haka suma fulanin.

Ku biyomu a kashi na biyu (2).
Hadejia A yau.

Wednesday, November 13, 2013

KASIDAR MALAMAN MAKARANTA.

Hadejia A yau! 1, Madallah da Mallam Usaini Sulaiman Malamin makaranta.

2, Bismillah mu fara da sunan Allah wanda yayi halittu, shi yayi malamin makaranta.

3, Allah shi ya shirya halitta, yayi ruwa wuta rana da wata yayi malaman Makaranta.

4, Shine yayi Malam Usaini, masu prince ta Eco banki kan hanyar zuwa Makabarta.

5, Sabo na gode sarki Allah, wanda ya bani iko na sa 'yata a Prince farar Makaranta.

6, Nagodewa Mallam Usaini, shine Headmastan Prince makarantar nan dana saka 'yata.

7, Ba shi dai ba har malamansa, koda zasu fishi hazaka sun isa malaman makaranta.

8, Nagodewa duk Malamansu, Yarinya a sati biyar ta haddace duk Jihohin kasata.

9, Ga jinjina ga Malam Usaini, da sauran Malamanda suke a Prince kuma kuna zuciyata.

10, Yarinya ta ban mamaki, tun daga A zuwa Zed idan ta zauna zata kawosu 'yata.

11, Lissafi kamar kalkuleta, kai ko kalkuleta ma nasan da kadan fa zatafi 'yata.

12, Burin duk Uba tarbiyya, to Alhamdulillahi Allah shi yayi malaman Makaranta.

13, Iyaye nai kira a gareku, duk mai Da ya kaishi Prince domin yaga fa'idar Makaranta.

14, Ga koyon Handwritting Idan Munje home work suke baiwa 'yata.

Tuesday, November 12, 2013

ZUWAN AMINU ALA HADEJIA.KADDAMARDA LITTAFIN WAKOKIN HARUNA UJI...

Aminu Ala.
Free Web Proxy

1, Mun gode Aminu Ala, Barka da zuwa Hadejia, gun taron kaddamar da littafin Aji kima.

2, Bismillah zana fara waka da yabon gwanina, gwanin kowa a waka lalle Ala babu dama.

3, Nagodewa Ilahi, Nagode Aminu Ala nagode Aji kima.

4, Ranar Asabat a fantai, A filin kaddamar da tarihin Haruna Uji, da wakoki nai masu dama.

5, Haruna Uji Hadejia, ya bada gudunmawa fa, a wakoki da suke kai sako ai nadama.

6, Ko anyi raha a watse, ko a fadakarda kai zaman rayuwarka ina makoma.

7, Taro kuma yayi kyawu, jama'a duk sunji dadi, suna yin jinjina gun shi wannan wanda yayi littafin Aji kima.

8, Ado Ahmed Gidan dabino, dashi da Aminu Ala, Bashir Ahmed blogger, Marubuta baku dama.

9, Yasir Ramadan gwale bai samu zuwa ba saboda nisa, Amma sakonka na san ya iske Aji kima.

10, In zaka fadi fadi gaskiya, wani shafi ne na Yasir, kaje kaga zunzurutun fasaha babu dama.

11, Godiya gun kungiyoyin, facebook na jihar jigawa, shugabannin Dandalin siyasa mun dau sakonku kuma.

12, Gizagawan zumunci, suma ba'a barsu baya, Dandalin marubuta godiya wakilancinku kuma.

13, Dr. Dahiru godiyarmu, bata manta da shi ba, don shine yayi sharhin littafin Aji kima.

14, Ga sakon godiyarmu ga Dr. Abbas na Ringim, shima ya danyi sharhi, jama'armu Ina makoma.

15, Shugaban karamar hukumar Hadejiya Alhajindo, Umar Danjani p.A. Barka da zuwanka kaima.

Alh. Baffa Bura.... Allah yayi ma Mabudi.......
Hadejia A yau.

Sunday, November 10, 2013

SAKON BANGAJIYA DAGA KWAMITIN KADDAMAR DA LITTAFIN TARIHIN HARUNA UJI DA WAKOKINSA.

Comrade Aji Kima Hadejia!
Free Web Proxy
HADEJIA A YAU!
Assalamu Alaikum! Bayan gaisuwa irinta Addinin Musulunci, muna meka sakon godiya da ban gajiya ga wadanda suka halarci taron kaddamar da Littafin Tarihin Marigayi Haruna Uji da Wakokinsa. Wanda akayi a
Ranar Asabat 9th November 2013, a Dakin Taro na sakandare fantai.

Muna Meka sakon bangajiya da fatan Alkairi zuwa ga Shugaban karamar hukumar Hadejia, Alh. Abba Haruna. Da mai baiwa Gwamna shawara akan harkokin dalibai Alh Umaru Danjani.

Gaisuwa da fatan Alkairi ga
Shugaban kwalejin Ilimi ta jihar Jigawa Dr. Dahiru Abdulkadir. Da shugaban Makarantar koyon aikin Alkalanci ta Ringim Dr. Abbas A. Abbas.

Gaisuwa da fatan Alkairi ga
Babban mai kaddamarwa;

Pharm.Hashim Ubale Yusufu

Muna meka sakon godiya ga kungiyoyin facebook da kuma kungiyoyin Marubuta da Mawallafa na Jihohin kano da jigawa.

Sakon godiya da bangajiya zuwa ga Alh Aminu Ladan Ala
da Ado Ahmed Gidan Dibino.

Muna Meka sakon Jinjina da bangajiya zuwa ga Alh Baffa Bura FNICPR.

Muna meka sakon Godiya ga Iyalan Marigayi Haruna Uji da jama'ar Unguwar Gandun Sarki.
Gaisuwa da godiya ga Jami'an tsaro da 'yan jarida da ma'aikatan yada Labarai.
Allah ya huci gajiya.

Tuesday, November 5, 2013

TARIHIN MARIGAYI HARUNA UJI DA WAKOKINSA. MUHD. AJI HADEJIA...

Comrade Aji Kima Hadejia!
Free Web Proxy
HADEJIA A YAU!
Muna gayyatar yan uwa da Abokan Arziki zuwa wajen kaddamar da littafin da na
rubuta wanda na kira
"Tarihin Alh Haruna Uji da Wakokinsa"

Za'ayi Taron kamar haka:

Rana=Asabat 9th November 2013 Guri=Dakin Taro na sakandire fantai Hadejia Jigawa state Lokaci=10am

Baban Bako na musamman;

mai girma gwamnan jihar jigawa Alhaji Dr sule Lamido con.

Uban Taro;

Mai Martaba sarkin Hadejia Alhaji Adamu Abubakar Maje Con.

Shugabannin Taro;

1.Alhaji Suleman Baffa
2.Alh Muhammadu Daguro

Masu Masaukin baki:

1.Mai girma shugaban karamar hukumar Hadejia Alh Abba Haruna
2.mai girma dan majalissar jiha mai wakiltar Hadejia Alh Aminu Abus
3.Mai girma mai bawa gwamna shawara akan harkokin dalibai Alh Umaru Danjani.

Bako mai jawabi;

Mai girma kwamishinan Ilimi na jihar Jigawa Farfesa Haruna Wakili.

Mai bitar Littafi;

Shugaban kwalejin Ilimi ta jihar Jigawa Dr. Dahiru Abdulkadir.

Babban mai kaddamarwa;

Pharm.Hashim Ubale Yusufu

Mataimakan masu kaddamarwa

1.Mai Girma shugaban jam'iyar PDP ta jihar Jigawa Alh Salisu Mamuda.
2.Mai Girma kakakin majalissar dokokin jihar jigawa Alh Adamu Ahmed
sarawa.
3.Mai Girma mataimakin kakakin majalissar dokoki Abdu Alh Dauda Karkarna.
4.Masu Girma Ciyamomin Hadejia da Auyo da k/Hausa da Kaugama da m/madori da Guri da birniwa daKirikasamma.
5.Masu Girma yan majalissar Hadejia, Auyo. K/hausa, Kaugama, M/madori da Guri da Birniwa da Kirikasamma
6.Mai Girma kwamishinan matasa da raya al'adun gargajiya Alh Babandi Muhammad.
7.Alhaji Salisu Sambajo MFR

Masu Rera Waka;

1.Alh Aminu Ladan Ala
2.Fati Niger
3.Saddiq zazzabi
4.Surajo mai Asharalle
5.Dan Kwamarado

Masu Gabatar da Taro

1.Alh Baffa Bura FNICPR
2.Alh Umar Kiyari Jitau Madamuwa
3.Salmanu Adamu Rishi.

Allah ya bada ikon Zuwa.

Tuesday, October 22, 2013

KA SAN KANKA DA KANKA! (TAMBAYOYI 50) DAGA HARUNA AMINU HARUNA.

Hadejia A yau!

Muna cikin wani zamani, da mutane, sunfi damuwa da bayani akan wasu fiye da kansu, sunfi binciko laifin wasu fiye da nasu


Sayyadina Umar yace kuyi wa kanku hisabi kafin ayi muku, Abubawanda suke jawo tsira, Bautawa Allah shi kadai da Iklasi, akan sunnar Manzon Allah, a cikin Akida, da Ibada, Da mu'amalah, da Halaye masu kyau, yiwa kanka tambaya, hamsin don kasan matsayinka :


Allah yasa mu dace :

1- waye ya yika ?

2- mai yasa ya yika ?

3- kai waye ?

4- A ina kake ?

5- mai kake yi ?

6- Ina zaka ?

7- mai zai faru ?

8- mai kafi so a rayuwarka ?

9- mai kafi ki rayuwarka?

10- Duk abinda kakeyi, kana da hujja a sharia?

11- su waye abokanka?

12- Yaya zamanka da iyayanka?

13- Yaya zamanka yake da iyalanka?

14- Wace kungiya kakeyi don me?

15- A kwai wani yanzu haka da bakwa shiri da shi?

16- Tsakaninka da Allah ka taba cin amanar wani?

17 Kanayin karya?

18- Kana Dun guma ashariya?

19- Yaya zamanaka da makotanka?

20- Wace shedar ilmi kake dauke da ita?

21- kana salloli a Jam'i musamman a masallaci?

22- yaya alakar ka da danginka take ?

23- shin kana sada zumunta?

24- shin kana bayar da sadaka ?

25- shin kana karanta Alkur'ani mai girma?

26- kana azumin litinin da Alhamis?

27- kana sallar Shafi'i da wuturi?

28- kana zuwa asibiti domin ziyarar marasa lafiya?

29- Kana yawan saba alkawari ?

30shin kana azumtar kwanaki masu haske, ranar
sha uku, sha hudu, sha biyar?

31- shin kana kiyamul- laili?

32-kana umarni da kyakyawa da hani da mummuna?

33- kana zuwa aiki akan kari kuma ka tashi akan lokaci?

34- kana zuwa gaban malami domin daukar karatu?

35-ka tabbatar abinda kake ci halal ne?

36- kana kuwa damuwa da halin da yan uwanka musulmi suke ciki?

37- kana taimaka marayu kuwa?

38- salati nawa kake yiwa Annabi saw kullum?

39- Istigfari nawa kakeyi kullum?

40- kana zuwa makabarta domin tuna lahira?

41- kana zuwa taaziyya da sallar Jana'iza?

42- ka taba yin kuka saboda tsoran Allah?

43- shin kana yiwa dukkan musulmi sallama ko
kuwa sai wanda ka sani?


44- kanayin rantsuwa akan karya kuwa?

45- kana shan taba ko wiwi ko giya ko hodar iblis?

46- kana jin kade- kade, da wake- wake?

47- kana aske gemunka?

48- ka taba karbar cin hanci?

49- kana kyautawa iyalanka?

50- kana gaba da wani kuwa?

Allah yasa mu dace.

Wednesday, September 18, 2013

CIWON KODA A KASAR HADEJIA! DAGA PHARM. HASHIM UBALE YUSUF.

Hadejia A yau! Daga pharmacy Hashim Ubale Yusufu


Bismillahir Rahmanir Rahim. Assalamu Alaikum.

CIWON KODA A KASAR HADEJIA: A bisa kididdiga, kimanin mutane miliyan talatin (30million) ne ke dauke da cutar Koda a tarayyar Nigeria. (National Association of Nephrology). Yawancin wadannan mutane na mutuwa kuwa katsam daga cutukan da suka shafi makwarar jini da zuciya, wanda ke da danganta da ciwon kodar. Wannan ya nuna cewa kimanin mutane ashirin bisa dari (20%) na ‘yan Nigeria na fama da wannan ciwo, wanda ana ganin alama daga yawan karuwar masu neman tace jini (dialysis). A wasu asibitocin zaka iske kimanin mutane 200 zuwa 300 ke zuwa neman tace jininsu a rana.



Cututtuka da dama na iya jawo ciwon Koda. Manyan dalilan dake hassada wannan ciwo anan karkarar sun hada da ciwo tsutsa (infections), kishirwa da kuma shaye shayen magunguna kai tsaye, Hawan Jini, shan taba da makamantansu.
Ita koda tana taimakawa jikine wajen tace dattin da kan taru a jikin mutum, sannan kuma tana taimakawa wajen tsotse ruwa, da sukari da sauran sinadaran gina jiki dake yawo a jini domin kar su bi fitsari su fice. Kenan zamu iya gani cewa idan har Koda bazata iya yin wannan tatar ba, to kuwa akwai matsala. Babban abun dazai faru kuwa shine, dattin na iya tare kofofin da jini da fitsari zasu bi, daga nan sai a fara kumbura, da kuma samun zazzafan ciwo na fitar hankali a hanyar da fitsari yake bi.




Sau tari zaka tarar mutane na aikin dake sa su zubad da gumi mai yawa, amma babu ruwa a kusa dasu. A kauyuka da rugage, zaka samu rijiyoyi sun kafe, ko kuma zasu sha ruwa gurbatacce, saboda ba inda zasu samu ruwan mai kyau su sha. Wannan bala’i ne.
Sannan kuma, yanzu wani abu wanda yake kamar gasa shine shaye shayen magunguna babu dalili ko kuma babu neman shawarar masana.




Wannan ka iyasa shan gurbatattun magunguna ko na jabu wadanda zasu iya cutar da ita kodar ta daina aiki. Haka kuma shaye shayen maganin gargajiya na daya daga cikin abubuwan da ke jawon wannan ciwo.
Akwai gazawar kayan aiki a asibitocinmu na tace jini da musayar koda, wanda hakan na jawo matsalar kai marasa lafiyar kasashen waje don warkarwa. A inda kuwa babu halin haka, sai addua kenan.

Tuesday, September 17, 2013

MARIGAYI SARKIN DOGARAI DA SAURAN MARIGAYA...

ALLAHU AKBAR! A Satinda ya Gabata ne Masarautar Hadejia tayi Rashi Bubba wanda Tarihi bazai Manta da wannan Rashi ba.


A cikin wadanda suka rasa rayukansu a sanadiyyar Hatsarin Mota a Hanyar Kano, Mutum goma sha daya ne! A wannan hoto kuma akwai Sarkin Dogarai da Galadiman Dogarai da Madakin Dogarai da Wamban Dogarai da Makaman Dogarai da Magayakin Dogarai da Garkuwan Dogarai da Chiroman Lema da Shitu Dogari da
Manu Mai Hoto.



Ya Allah Muna Rokonka da sunayenka tsarkaka Allah ka Gafarta musu. Amin.
Hadejia A yau!

SARKIN DOGARAN HADEJIA
Free Web Proxy
WAMBAN DOGARAI.Free Web Proxy
Galadiman Dogarai Free Web ProxyMadakin DogaraiFree Web ProxyFree Web Proxy Free Web ProxyImage Hosted by ImageTitan.com[URL="http://img4.imagetitan.com/img4/small/8/8_s.dogarai.jpg" border=0 alt="Image Hosted by ImageTitan.com">Image Hosted by ImageTitan.com KOLI DIREBA
Free Web Proxy SHITU DOGARI
Free Web Proxy

Sunday, September 8, 2013

****TAURARINMU HADEJIAWA PART SIX(6)****

Free Web Proxy
Hadejia A yau.. Daga Muhammad Idris.
A ci gaba da kawo muku Tarihin wadanda Suka baiwa Kasar Hadejia Gudunmawa, yau Mun Tabo kadan daga Tarihin Marigayi Shatiman Hadejia Alh. Hassan Abbas.
****SHATIMAN HADEJIA ALHAJI HASAN ABBAS*****

Marigayi Shatiman Hadejia yana daya daga cikin dattijan arewa,manya a jihar kano da jigawa.Ya fara aiki tun daga Native Authority(NA) daga nan ya koma tarayya.Ya rike mukamin karamin ministan fetur a zamanin IBB. Shatiman Hadejia mutum ne mai kishin kasa da rikon addini. Shi ne sanadin aikin mutane da yawa a kaduna kuma har ya rasu akwai mutane da dama a zaune a gidansa.


Shatima ne ya fara gina katafaren gida domin saukar bakin kunya a Hadejia. Shi ya dauki dawainiyar
gyaran masallacin juma'a na lokaci mai tsawo.


Ya dauki nauyin sayen likkafani ga mamata har tsawon rayuwarsa. Arzik insa ya amfani 'yan uwa da sauran jama'a matuka domin akwai wadanda ya dauki nauyin ba su albashi har ya koma ga Allah subhanahu wa ta'ala.Muna addu'a Allah subhanahu wa ta'ala ya ji kansa ya albarkanci zuriyarsa.
Daga Muhammad Idris.

Wednesday, August 28, 2013

DANGANTAKA TSAKANIN BIRNI DA KAUYUKAN KASAR HADEJIA. DAGA M. HUSAINI SHEHU..

Hadejia A yau!
Daga M. Hussaini Shehu


DANGANTAKAR BIRNI DA KAUYE

Dangantaka tsakanin birni da kauye a kasarmu ta Hadejia tanada tsohon tarishi. Yana da wuyar gaske kasami bahadeje ko bahadejiya dake birni ko kauye da bashi da gidan yan’uwa ko gonar gado a daya daga wadannan wurare dana ambata.DA

Bukukuwan sallah-: shekarun baya zakaga kowane gida cike da baki yan’uwanmu na kauye sunzo cikin Hadejia domin sada zumunci da juna da kuma kallon buku kuwan sallah.

Wannan al’ada tamu tataimaka wa kasarmu sosai wajen jaddada hadinkai a tsakaninmu , kuma tataimaka wajen kawarda kyama tsakanin junanmu. Yanzu a wannan zamani irin wannan kyakkawar al’ada tamu tazama tarishi, sai ayi bukukuwan sallah a
gama bazakaga kowa a gidajenmuba. Kai koda wakilan kananan hukumominmu dawuya kasami guda uku daga cikin takwas sunzo domin sada zumunci kamar yadda akeyi a shekarun baya.


Kuma abin mamaki saika iske sauran masarautu bahaka sukeba, zakaga kowane shugaban karamar hukuma yazo sun hallara domin tattauna matsalolin wannan masarauta.




Shin minene yajawo
hakan? Nomi jide-: Inna tsammanin wannan al’ada tamu itace tasa ake cemana “Hadejia tsintsiya madaurinki daya”. Watau dadama daga cikin mutanan dake cikin Birnin Hadejia a shekarun baya sunada gidajensu nagado dakuma gonaki a kauyuka, aduk lokacinda damina ta sauka sukan koma gidajensu dake kauyuka
domin yin noma. Bazasu dawo gariba sai bayan damina. Zan iya tunawa mahaifina wata shekara muna shira game da wannan dabia tamu, sai yace mini: aduk cikin lokonmu gidanmune kawai yake ragewa da mutane idan damina ta sauka. Sauran makwabta kowa yakan koma kauye dominyin noma.


Saboda haka yan’uwa tayaya idanba hudubar shedanba zamu banbanta mutumun birni da kauye? Amsata shine duk mutumin kauyen Hadejia Dan Garin Hadejia ne sannan kuma duk mutumin Birnin Hadejia dan kauyen Hadejiane.


Tambaya anan itace idan Maganar danayi a baya gaskiyace, shin akwai maana idan mukayi maganar rabuwar kawuna tsakanin mutumin kauye dana birni?


Ga-manda-: wannanma wata tsohuwar al’adace tamu ta Hadejiawa da take kara nuna mana karfin dangan taka tsakanin kauye da birni. Bayan al’adar Nomu jide wanda kamar yadda nafadi a baya take nufin zuwa kauyukanmu da damina donyin noma, idan mungirbe mu kwaso amfanin zuwa gidajenmu na birni. Ha’ilayau mutumin birni musamman ma Mata sukan je ziyarar yan’uwa kauyu kammu bayan an kawo amfanin gona gida.


Ayayinda zasu tafi sukanyi guzurin
kayan miya wanda baa fiya samunsu a karkaraba, sukuma ayayin da suka gama zayararsu, yan’uwanmu na kauye sukan basu
amfanin gona kamar su: gero, dawa, wake dadai sauransu domin yin guzuri. Inna tsammanin wannan alada tamu haryanzu tananan anayinta tsakaninmu, to kaga kuwa ashe idan akwai wadannan dagantaka to ashe gaba dayanmu Hadejiawa yan’uwan junane. Saboda haka miye dalilin rabe raben kawuna tsakanin kauye da birni?




Sarauta-: Kowa yasani Sarautarmu ta Hadejia dama ta sauran kasashen Hausa ana nada Mai sarauta watau hakimi ko dagaci daga cikin yayan sarakai dake cikin gari a turasu kauyukammu domin yin mulki. Sannan ayayin
da hakimi zai tare kasarsa yakan tafi da sauran yaransa wadanda zasu tayashi mulki yazuwa kauye. Kuma dadama daga cikinsu idan sukaje zasu auri mata acan daganan sunzama yan can kauyen.


Shiyasa duk wani mai sarauta ko yaran mai sarauta a kauye idan aka binciki tarishinsu zaka iske zuwa yayi tare da hakiminsa ko dagacinsa Watau mutumin birnin Hadejiane, musamman ma da ya kasance al’adarmu ta Hadejiawa ta banbanta data Kanawa maana duk wanda fada ta tura kauye domin wakilci to zai zauna ne dindindin watau babu canji. Shiyasa idan shekaru sukayi yawa bama iya gane cewar zuwa mukayi donyin sarauta ba a nan muke ba shekarun baya. To amma abin mamaki saika iske yaron hakimi ko dagaci yana korafin nuna banbanci tsakanin birni da kauye. Shin akwai ma'ana a wannan dabia?


Allah yasa mugane.