HADEJIA A YAU! Wannan Dandali Na kirkireshi don bada Tarihin Kasar Hadejia, da Tarihin Sarakunan ta, da wadanda suka bada Gudunmawa wajen Inganta Al'adun Gargajiya. Hadejia A yau. Ismailasabo@gmail.com
Saturday, January 31, 2015
HISTORY OF BARIKIN HADEJIA...
Monday, January 26, 2015
TARIHIN KAFUWAR GARIN MAIRAKUMI.
- Garin Mairakumi ya kafu ne a zamanin Sarkin fulanin Hadejia Umaru, a lokacin da Sarkin Hadejia Sambo ya karbo Tutar Jaddada Musulunci bai zauna a Garin Hadejia ba saboda yana gurbin shehu don Neman Ilmi. Bayan Sambo yayi niyyar dawowa Kasar Hadejia sai ya nemi alfarma ga Shehu don yana so ya zauna a Wajen Hadejia, domin ya samu damar kiwon Dabbobinsa da kuma bayar da Ilmi ga Almajiransa, sai Shehu yace masa to idan yaje garin Hadejia a Arewa da Hadejia in ya ketare jigawa guda Hudu to anan akwai wani Daji mai ciyawa dabbobi zasu samu abinci a dajin. Sambo yayi Bankwana da Shehu ya taho kasar Hadejia.
Saturday, January 10, 2015
TARIHIN RAYUWAR ALH. SHU'AIBU HARUNA.
ALHAJI SHU'AIBU HARUNA HADEJIA.
Saturday, December 20, 2014
ZIYARA DA AMFANINTA.
r">Ziyara wani Nau'i ne na zumunci wanda mutane suke aiwatar da ita domin sada zumunci ga 'yan'uwa da abokan Arziki. zumunci wata irin halayya ce ta kwarai wacce ke sadar da dangantaka ta nasaba tsakanin ’yan'uwa ko bare. Zumunci ne ke kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali da fahimtar juna tsakanin al’umma.
Ta hanyoyin da mutum zai bi ya inganta zumunci shine, kaiwa ziyara ga 'yan'uwansa kamar kaka, uba kokuma kanin mahaifi ko kanin mahaifiya da sauransu. Ta haka ne mutum zai gane irin yadda Alaqarsa take da 'yan uwansa na nesa ko na kusa. Haka kuma kowa yana da iya kimar zumuncin da zai gudanar a tsakaninsa da wani. Kamar yadda Hausawa suka ce zumunta a kafa take, to wannan gaskiya ne,domin
kuwa daya daga cikin manyan ginshikan zumunta shi ne ziyartar juna. Idan ka kula da zumunci shike sa mutum ya niki gari zuwa gidan abokinka ko wani dan'uwanka, ko bare musamman domin ganin yadda yake. Wannan ziyara kawai, ita ke haddasa kauna da mutunci mai dorewa a tsakanin al’umma.
A shekarun baya kamar shekara kamar goma zuwa sama,saboda muhimmancin ranar Juma'a,iyaye sukan je da 'ya'yansu gidajen 'yan'uwansu da Abokan Arziki domin gaisawa wanda hakan yana nuna ana nusar da yara ne da kaiwa ziyara ga 'yan uwansu. Harma yara suke kiran wannan ziyara da yawon Juma'a. Amma saboda shagaltar da zuciya irin ta shaidan tasa wannan kyakkyawan Aiki na ziyara ya fara ja baya ga yara harma da manyan a wannan zamani,domin shi bubba yana tunanin ai in yaje zai bada kudi, sannan yaro yana tunanin kar yaje ba'a bashi kudi ba.
Wednesday, December 3, 2014
TAKAITACCEN TARIHIN HASHIM UBALE YUSUF..
Wednesday, October 29, 2014
HADEJIA TOWN WALLS AND GATES.




HADEJIA TOWN WALLS AND GATES "Hadejia was a large town with 5 town gates and excellent walls about 30ft (9.14m) high, and 30ft (9.14m) thick " (Captain Philips 1909) Monday, September 29, 2014
TARIHIN RAYUWAR GALADIMAN KANO A TAKAICE! Alhaji Tijjani Hashim.
A shekarar 1952 Galadiman kano ya fara aiki a hukumar N. A. (Native Authority) ta Kano a matsayin Malamin Dabbobi, mai kula da tsafta da lafiyar dabbobi. A 1956 aka zabe shi a matsayin dan majalissa mai wakiltar Sumaila a majalisar dokoki ta Arewa dake kaduna.
A zaman sa a wannan majalisa ne ya rike mukamai da dama ciki har da shugaban hukumar bada kwangila ta Kaduna sannan ya rike shugaban kwamitin tabbatar da jamiyyar NPC ta lashe zabe a lardin Sardauna. Sannan ya rike mukamin Ministan Ayyukan cikin gida na Jihar Arewa. Yayi Kwamishinan lardi mai kula Lardin Kabba wandda yana kan wannan mukamin ne sojoji suka yi juyin mulki.
Bayan ya dawo gida sai Sarkin Kano Ado Bayero ya nada shi sarautar Dan-isan Kano kuma kansila mai kula da ayyukan gayya da taimakon kai da kai.
A cikin shekarar 1976 ne ya samu karin girma zuwa sarautar Turakin Kano da bashi kulawa da gundumar Kumbotso. sannan A 1980, ya sami canji zuwa kansila marar ofis saboda yawan harkokinsa na kasuwanci. A shekarar 1989, ya samu karin girma zuwa sarautar Dan-iyan Kano, kuma ya ci gaba rike mukamin kansila marar ofis.
A shekarar 1992, ya samu karin girma a sarauta inda aka nadashi Galadiman Kano kuma shugaban kwamitin kudi na majalisar Sarki. A shekarar 2012 Sarki ya kara masa aikin hakimcin birnin Kano. Wannan aiki ya ke rike dashi har Allah ya masa rasuwa.
Galadiman Kano Tijjani mutum ne mai hakuri da juriya da Alkairi. Kuma yana da daraja a Idanun mtane sakamakon amfani da yayi da damarsa ya kafa mutane a Gwamnati. kuma babu inda zai nemi Alfarma a gwamnati bai samu ba, wannan tasa ake masa Laqabi da GAJERE WAN GWAMNATI.
A ranar28/september/2014, Allah ya yiwa Galadiman kano rasuwa ya rasu ya bar 'ya'ya da Matan Aure da 'yan-uwa da dama. Muna Addu'a Allah ya gafarta masa.
Friday, August 15, 2014
TARIHIN DAN-AMAR DIN HADEJIA M. USMAN GINSAU.
Monday, March 17, 2014
TARIHIN JARMAN HADEJIA ALH. ABBA SAMBO (DAGA NA GABA PART FIVE 5)
Daga Muhammad Yawale.
Wasu ayyuka da yayi:
Thursday, March 6, 2014
TAURARINMU HADEJIAWA (Part four 4)
Saturday, March 1, 2014
DAGA NA GABA! HADEJIAWA (PART TWO 2)
Wednesday, February 19, 2014
DAGA NA GABA! HADEJIAWA...(part one 1)

;
Wednesday, February 5, 2014
EMIRE OF HADEJIA ALH.HARUNA ABDULKADIR.
But while previously, during colonial period, the Tafida administered Kafin Hausa as district head, until more recently when it was given to Chiroma, a son to the Emir. Fallowing Chiroma’s appointment as a chairman of the Kano state local government service commission he was unfortunately obliged to reside at Kano city, leaving Kafin Hausa to be administered by his deputy while he retain the title.
The old emirate council from 1971 – 1975meet more frequently under the chairmanship of the Galadima Yusuf and Adamu, the major responsibilities of that administration rested firmly with Dan’iya,M. abdulkadir Maidugu, himself a grandson a grand of the Emir Abdulkadir and formally Sarkin Auyo and district head of Auyo, he represented HADEJIA inthe Federal House of Assembly. In his return after the abolition of a civilian rule, he was appointed Senior Executive Councillor of the Emirate council in charge of finance, the native administration,works, rural water supplyand community development.
TheTafida alh. Abdulkadir Maigari, another grandson of the emir Abdulkadir was appointed a councillor in charge of Agric and Natural resourses.The Danburan muhammadu Hurdi……………….
.(Culled from “Local Government at Hadejiia 1977” By M. G. Smith)
By Ma'aji I Abubakar.
Monday, January 13, 2014
HAWAN SALLAR GANI (MAULUDI) A HADEJIA 13/01/2014.
Monday, December 30, 2013
TARIHIN KAFUWAR HADEJIA A TAKAICE..
Sunday, December 1, 2013
TARIHIN GIZMAWA (NGZIM) DA AL'ADUNSU.
GIZMAWA KO NGZIM. Wani sashe ne na Kanuri (Bare-bari) wadanda sukazo daga Borno. Kanuri dai sun kasu gida uku (3), akwai:
Mangawa
Gizmawa
da Larawa.
Mangawa Akasarinsu anfi samunsu a kasar Birniwa da Kirikasamma.
Gizmawa ana samunsu mafi yawa a kasar Guri. A garuruwa irin su Guri, Arin, Dagana, Joriyo, Adiyani, Zugo, Wacakal, Garmaguwa, Garbagal, Margadu,Tukuikui, Dole, Abir da sauransu.
Larawa kuma sunfi yawa a tsakanin Badar, Jigawa, da Bauchi ta kasar Guri. Ana samunsu a Garuruwa irin su: Takazza, Damegi, Gaduwa, Musari da sauransu.
Banbancin da ke tsakanin Gizmawa da Mangawa da Larawa bash da yawa. Kamar banbancin Hausar kano ne da ta katsina ko Hausar sokoto da ta Hadejia. Amma ko wanne yana fahimtar kowane tsakaninsu, wato banbancin a karin harshe ne, kuma a haka suke gane wannan kabilar Ba gizme ne ko Bamange.
Su kuma Kanurin Kadira sun sha bam ban da Gizmawa Larawa da Mangawa. Domin su suna Barbarci ne irin na Borno. Saboda haka ko tsarin zamantakewarsu da sarautarsu ya sha banban.
A bangaren al'adu da zamantakewa basu da bambanci da juna. (Gizmawa Mangawa da Larawa). Tsarin Addinin Musulunci da cudanya da Hausawa ta sa Al'adu da dama na Gizmawa sunyi watsi dasu. Kamar kidan Bango; Rawar Dimas; Rawar biki da al'adun Aurensu duka yanzu ba sosai ake yinsu ba da yawa Hausa ta kwace su.
Wani zaiyi tambaya me yasa aka samu kashe kashen kanuri har gida uku? Dalili shine, zamantakewa da ta bambanta aka samu watsuwarsu a kasar Hausa.
Rabewar Daular Kanem-Borno da Zuwan Rabeh ne yasa wasu daga cikinsu suka tsinci kansu a Daular Usmaniyya, wadda take cike da Hausa Fulani. Kanurinda suke yankin Masarautar Hadejia Musamman ma kasar Guri, sun gauraya da Badawa da fulani da Auyakawa. Hakan tasa karin sautin muryarsu ya sha bamban da kanurin Borno da Yobe. Sannan Al'adunsu sun jirwaye da na Hausawa.
Sannan tsarin Sarautarsu yasa dole suke Amfani da Bulama Maimakon Mai ko Lawan. Amma kuma har yanzu a garin Kadira zaka Iske Kanuri ne suke rike da sarautar garin tare da Badawa da kuma Hausa-fulani kadan.
Sannan ba'a iya bambance Bagizme ko Bamange ko Balare a fuska, domin daga cikinsu zaka iya samun Abubuwa kamar haka:-
*Zube (zane)
*Sutura
*Karin harshe
*Al'adun Aure
*Sana'a
*Tsarin Auratayya
*Addini
*Zamantakewa
*Sunaye
*Son girma
*Kishin yare
*Gardama
*Bajinta
*Ki fadi.
Zane a fuska ya danganta da tsarin iyayen mutum, wadansu iyayen suna da Sha'awar a yiwa 'ya'yansu zube, wasu ko basu da ra'ayin hakan. Saboda haka a cikinsu ana samun mai zube ana samun marar zube.
Barebari ______ Borno
Bamange______ Kirikasamma
Birniwa.
Bagizme________ Guri, Adiyani, Zugo, Gabargal.da sauransu.
Balare__________ Gaduwa, Musari, Takazza, Margadu.da sauransu.
Hadejia A yau.
Sunday, November 24, 2013
TARIHIN HARUNA UJI DA WAKOKINSA. KASHI NA BIYU (2).
Littafin Muhd. Aji Hadejia.
A kashi na farko kunji cewa Alh. Haruna Uji ya ci gaba da kidan Gurmi gadan gadan.
A lokacin Gwamnan Kano Abdu Bako, sai yaji labarin Haruna Uji, sai yasa aka nemoshi domin yayi masa waka akan wayar da kan Al'umma akan Noma. Saboda haka Gwamna Abdu Bako sai ya hadawa Haruna Uji kayan wasa, kamar Amsa Kuwwa (Loud speaker) da Abin Magana wato (Microphone) da Injin wuta, wato Generator.
Wannan shine lokaci na farko da Haruna Uji ya fara waka da kayan wasa na zamani, kuma ya kama yin waka gadan gadan a matsayin sana'a.
Wakar da yayi a lokacin Itace wakar Noma. Anyi wakar ne da nufin wayar da kan Talakawa su koma Aikin gona.
3.0. WAKOKIN HARUNA UJI NA FARKO.
Alh. Haruna Uji yayi wakoki masu tarin yawa, kuma a cikin Jerin wakokinsa ga wasu daga cikin wakokin da ya fara yi.
*Wakar Naira da kwabo sabon kudi.
*Wakar Gudaliya.
*Wakar Shamuwa.
*Wakar Noma.
*Wakar Bakar Rama.
Wadannan sune kusan Shahararrun wakokin da ya fara yi.
3.1. Ajin Haruna Uji a tsakanin Mawakan baka.
A cikin wani Littafi da Ibrahim Yaro Yahya da Abba Rufa'i suka tsara, Mamuda Aminu ya kawo rabe-raben Mawakan baka zuwa rukunai kamar haka:
*Mawakan Sarakuna
*Mawakan 'yan mata
*Mawakan Jama'a
*Mawakan Mafarauta. Da sauransu.
Ya kawo misalin Mawakan Jama'a shine wanda zai yiwa Sarakuna da 'yan kasuwa da 'yan mata da Masu kudi da talakawa waka. Misali Mamman shata da Haruna Uji da sauransu.
Hakan ta nuna cewa Haruna Uji ya kasance a cikin Mawakan Jama'a, domin ya tabo duk abinda aka zayyana a sama. Wato yakan yiwa kowa waka.
3.1.1 Dangantakar Haruna Uji da Mawakan Baka.
Alh. Haruna Uji yana da kyakkyawar dangantaka da sauran 'yan uwansa mawakan baka, yana girmamasu shima suna girmama shi, sannan ya hori wasu suma sun zama shahararrun mawaka a kasar Hausa. Yayiwa wasu waka kuma shima wasu sunyi masa. A cikin mawakan da suka masa waka har da Alh. Mamman shata, kuma shima Haruna Uji yayi wa Alh. Garba sufa wakar Ta'aziyya bayan ya mutu.
3.1.2 Jerin wasu daga wakokin Haruna Uji.
Bayan rukunin wakokinsa na farko, ga wasu daga cikin wakokin da yayi.
*Wakar Dankabo
*Wakar Alh. Sani Likori
*Wakar Direban Chiyaman
*Wakar (Air vice marshal) Ibrahim Alpha
*Wakar (kwamishinan 'yan sanda) Daudu Gwalalo
*Wakar Haruna karamba
*Wakar Adamu Hassan Abunabo
*Wakar Ahmed Aruwa
*Wakar Asabe Madara
*Wakar Amadu koloji makwallah
*Wakar Bako Inusa kano
*Wakar Balaraba
*Wakar Jimmai Aljummah
*Wakar Birgediya Abdullahi shalin.
*Wakar Dankamasho
*Wakar Fulanin Jebbi fulato
*Wakar Idiyo Mai kayan Babur
*Wakar Kainuwa.
SAURAN WAKOKIN KU DUBA LITTAFIN.
Ka duba kashi na uku (3)
Thursday, November 21, 2013
TARIHIN HARUNA UJI. DA WAKOKINSA. KASHI NA DAYA (1).
Hadejia A yau! An haifi Alh. Haruna Uji A Unguwar Gandun sarki dake cikin garin Hadejia, a shekarar (1946). Sunan Mahaifinsa Mallam Ibrahim, Malami ne kuma shine Limamin Gandun sarki. Sunan Mahaifiyarsa Zainabu itama mutumiyar Unguwar ce. Anan ya tashi yayi wayo. Yana kimanin shekara shida mahaifinsa ya sakashi a makarantar Allo dake kofar gidansu, a gun wani Malami da ake kira Mallam Alhaji.
Haruna Uji ya shafe wajen shekaru uku yana wannan Makaranta a Gandun sarki, daga nan suka tashi da malaminsa zuwa garin Birniwa wanda take gabas da Hadejia, mai nisan kilo mita 45. Sun kwashe shekaru kamar biyu suna karatu da sauran Almajirai, anan Uji ya samu karatu mai dama.
Bayan nan suka bar Birniwa suka dawo Hadejia suka ci gaba da karatu a Gandun sarki. Wannan yasa ya samu karatu mai dama fiye da sauran yara musamman wadanda suka zauna a gida basu fita wani guri neman Ilmi ba. A wannan lokaci Mallam Alhaji yakan sa Uji ya kula da yara tare da koya musu karatu. Haruna Uji ya bar makarantar Allo yana dan shekara goma sha biyu, bayan ya samu karatu mai dama.
Hadejia A yau!
1.1, ASALIN INKIYAR HARUNA UJI..
Sunansa na yanka Haruna, yaci sunan wan Mahaifinsa, wato Mallam Haruna. Mallam Haruna mai sunan Uji yana da mata mai suna IYA KURA, Lokacin Uji yana karami matan kanin Babansa suna masa wasa suna ce masa Mijin Iya Kura, Mijin Iya Kura' A wannan Lokacin yara kannensa basu da baki, sai suke ce masa, Ujin Iya Kura. Maimakon Mijin Iya Kura. Wannan shine Asalin inda Haruna Uji ya samo Inkiyar Uji. Tun ana danganta sunan da Iya Kura har aka daina ake cewa Uji.
1.11, SIFFAR HARUNA UJI.
Haruna Uji baki ne, mai matsakaicin tsawo, yana da jiki matsakaici, ga farin hakora da bakin gashi, yana yawan barin gashin baki, ga magana (Idanu) haka kuma, ma'abocin barin suma ne, yana da Murya mai zaki da kauri kadan, kuma Gwanin Ado ne, da manyan kaya na sarauta. Kuma yakan saka 'yar shara, musamman lokacin zafi.
Alh. Haruna Uji mutum nd mai fara'a da kyauta, domin abin hannunsa bai rufe masa ido ba. Yana da raha sannan kuma bashi da wata nakasa a fili.
2.0, SANA'OIN HARUNA UJI..
2.1, Farauta da Noma.
Bayan Haruna Uji ya bar makarantar Allo, ya fara zuwa Daji da nufin farauta. Wadda itace sana'arsa ta farko, wanda ya fara, kuma ta sanyashi jarunta inda ya zama bashi da tsoro. Kuma a nan ne ya samu tambaya wato lakani na tsare kai.
Bayan farauta Haruna Uji Manomi ne, ya fara aikin gona ne da taya mahaifinsa, domin neman tabariki, wannan tasa yasan harkar noma wanda har yake noma gonar kansa.
2.2, Sana'ar Tukin Mota (Direba)
Alh. Haruna Uji yayi Sana'ar Tukin mota, wanda ya fara da Yaron mota a gun Mai gidansa wanda ake kira da suna Jibrin Dan Amingo. Jibrin Dan Amingo dan Asalin Danbatta ne ta Jihar Kano. Haruna Uji ya shafe shekaru da dama yana sana'ar yaron mota. Tukin mota ne sana'arsa ta farko da ta fara fitar dashi wani gari da nufin zama. Suna aiki ne tsakanin Kano da Hadejia.
Kuma a wannan lokacin suna zaune ne a garin kano a Tudun wada. Amma duk abinda ya taso a gida dashi akeyi, musamman aikin gona da bukukuwa da sauransu.
2.3, Sana'ar Waka.
Haruna Uji bai gaji waka ba, domin Mahaifinsa Malami ne, kuma ko a wakarsa ta Gurmi ba Haramun ba yana cewa:-
"Ni Haruna dan Mallam nake, Waka ta ba ta gado bace"
Saboda haka tun farko Haruna Uji ya riki waka ne a matsayin nishadi, domin ba wanda ya koya masa waka a matsayin Sana'a.
Haruna Uji ya fara ganin Gurmi ne a gun wani ma'aikacin titi wanda sukayi aiki a hanyar Mallam madori zuwa Gumel, wanda ake kira Dan-mato, a gun Dan-mato Uji ya fara ganin Gurmi da kidansa, shi Dan-mato yana kada Gurmi ne a yayinda suka samu hutun aiki. Yana kadawa yana waka, lokacin Uji yana Matashi, duk lokacinda sukaje kallon aiki sai su tsaya suna ganin kidan Gurmin Dan-mato, wannan tasa kidan Gurmi ya shiga ran Haruna Uji, idan ya dawo gida sai yakan nemi gwangwani da tsirkiya ya hada Gurmi yana kadawa. Har Dan-mato suka hada aikin hanya bai koyawa Uji Gurmi ba, sai dai Uji yana zuwa yana ganin yanda yake kadawa. Wannan tasa Uji ya dinga kwaikoyon Dan-mato tun bai iya ba har ya koya.
Wannan yasa idan yana gurmi yara sukan tsaya suna ji da kallonsa, Wannan shine Asalin koyon Gurmin Haruna Uji. Daga nan sai ya fara tunanin ya samu sanda, da lilo da butar Duma da fatar Damo da Zobe domin ya hada bubban Gurmi.
Farkon lokacinda ya fara Gurmi idan an bashi abu baya karba, don yanayi ne saboda Nishadi. Kuma sau da yawa idan ya fito hira ko ana wani biki na samari da 'yan mata, yakan kada Gurminsa yana waka, samari da 'yan mata suna kallo.
A wancan lokacin yana Gurmi yana aikin Mota, wannan yasa ya fara Gurmi a garuruwa daban daban na Arewacin Nigeria.
Daga nan Uji ya bar tukin mota ya koma kidan Gurmi Kuma ya nemi mataimaka don sunayi su biyu.
Karashe a kashi na 2.
Littafin Muhd. Aji Hadejia
Tuesday, November 19, 2013
ZAMANTAKEWA TSAKANIN MANOMA DA MAKIYAYA A KUDANCIN GURI. (KASHI NA 2)
BY COMRADE GARBA MUHD HADEJIA
Sunday, November 17, 2013
ZAMANTAKEWA TSAKANIN MANOMA DA MAKIYAYA A KUDANCIN GURI...(1)
Hadejia A yau! Daga Garba Muhammad Hadejia....
Ku biyomu a kashi na biyu (2).
Hadejia A yau.
Wednesday, November 13, 2013
KASIDAR MALAMAN MAKARANTA.
2, Bismillah mu fara da sunan Allah wanda yayi halittu, shi yayi malamin makaranta.
3, Allah shi ya shirya halitta, yayi ruwa wuta rana da wata yayi malaman Makaranta.
4, Shine yayi Malam Usaini, masu prince ta Eco banki kan hanyar zuwa Makabarta.
5, Sabo na gode sarki Allah, wanda ya bani iko na sa 'yata a Prince farar Makaranta.
6, Nagodewa Mallam Usaini, shine Headmastan Prince makarantar nan dana saka 'yata.
7, Ba shi dai ba har malamansa, koda zasu fishi hazaka sun isa malaman makaranta.
8, Nagodewa duk Malamansu, Yarinya a sati biyar ta haddace duk Jihohin kasata.
9, Ga jinjina ga Malam Usaini, da sauran Malamanda suke a Prince kuma kuna zuciyata.
10, Yarinya ta ban mamaki, tun daga A zuwa Zed idan ta zauna zata kawosu 'yata.
11, Lissafi kamar kalkuleta, kai ko kalkuleta ma nasan da kadan fa zatafi 'yata.
12, Burin duk Uba tarbiyya, to Alhamdulillahi Allah shi yayi malaman Makaranta.
13, Iyaye nai kira a gareku, duk mai Da ya kaishi Prince domin yaga fa'idar Makaranta.
14, Ga koyon Handwritting Idan Munje home work suke baiwa 'yata.
Tuesday, November 12, 2013
ZUWAN AMINU ALA HADEJIA.KADDAMARDA LITTAFIN WAKOKIN HARUNA UJI...
1, Mun gode Aminu Ala, Barka da zuwa Hadejia, gun taron kaddamar da littafin Aji kima.
2, Bismillah zana fara waka da yabon gwanina, gwanin kowa a waka lalle Ala babu dama.
3, Nagodewa Ilahi, Nagode Aminu Ala nagode Aji kima.
4, Ranar Asabat a fantai, A filin kaddamar da tarihin Haruna Uji, da wakoki nai masu dama.
5, Haruna Uji Hadejia, ya bada gudunmawa fa, a wakoki da suke kai sako ai nadama.
6, Ko anyi raha a watse, ko a fadakarda kai zaman rayuwarka ina makoma.
7, Taro kuma yayi kyawu, jama'a duk sunji dadi, suna yin jinjina gun shi wannan wanda yayi littafin Aji kima.
8, Ado Ahmed Gidan dabino, dashi da Aminu Ala, Bashir Ahmed blogger, Marubuta baku dama.
9, Yasir Ramadan gwale bai samu zuwa ba saboda nisa, Amma sakonka na san ya iske Aji kima.
10, In zaka fadi fadi gaskiya, wani shafi ne na Yasir, kaje kaga zunzurutun fasaha babu dama.
11, Godiya gun kungiyoyin, facebook na jihar jigawa, shugabannin Dandalin siyasa mun dau sakonku kuma.
12, Gizagawan zumunci, suma ba'a barsu baya, Dandalin marubuta godiya wakilancinku kuma.
13, Dr. Dahiru godiyarmu, bata manta da shi ba, don shine yayi sharhin littafin Aji kima.
14, Ga sakon godiyarmu ga Dr. Abbas na Ringim, shima ya danyi sharhi, jama'armu Ina makoma.
15, Shugaban karamar hukumar Hadejiya Alhajindo, Umar Danjani p.A. Barka da zuwanka kaima.
Alh. Baffa Bura.... Allah yayi ma Mabudi.......
Hadejia A yau.
Sunday, November 10, 2013
SAKON BANGAJIYA DAGA KWAMITIN KADDAMAR DA LITTAFIN TARIHIN HARUNA UJI DA WAKOKINSA.
HADEJIA A YAU!
Assalamu Alaikum! Bayan gaisuwa irinta Addinin Musulunci, muna meka sakon godiya da ban gajiya ga wadanda suka halarci taron kaddamar da Littafin Tarihin Marigayi Haruna Uji da Wakokinsa. Wanda akayi a
Ranar Asabat 9th November 2013, a Dakin Taro na sakandare fantai.
Muna Meka sakon bangajiya da fatan Alkairi zuwa ga Shugaban karamar hukumar Hadejia, Alh. Abba Haruna. Da mai baiwa Gwamna shawara akan harkokin dalibai Alh Umaru Danjani.
Gaisuwa da fatan Alkairi ga
Shugaban kwalejin Ilimi ta jihar Jigawa Dr. Dahiru Abdulkadir. Da shugaban Makarantar koyon aikin Alkalanci ta Ringim Dr. Abbas A. Abbas.
Gaisuwa da fatan Alkairi ga
Babban mai kaddamarwa;
Pharm.Hashim Ubale Yusufu
Muna meka sakon godiya ga kungiyoyin facebook da kuma kungiyoyin Marubuta da Mawallafa na Jihohin kano da jigawa.
Sakon godiya da bangajiya zuwa ga Alh Aminu Ladan Ala
da Ado Ahmed Gidan Dibino.
Muna Meka sakon Jinjina da bangajiya zuwa ga Alh Baffa Bura FNICPR.
Muna meka sakon Godiya ga Iyalan Marigayi Haruna Uji da jama'ar Unguwar Gandun Sarki.
Gaisuwa da godiya ga Jami'an tsaro da 'yan jarida da ma'aikatan yada Labarai.
Allah ya huci gajiya.
Tuesday, November 5, 2013
TARIHIN MARIGAYI HARUNA UJI DA WAKOKINSA. MUHD. AJI HADEJIA...
HADEJIA A YAU!
Muna gayyatar yan uwa da Abokan Arziki zuwa wajen kaddamar da littafin da na
rubuta wanda na kira
"Tarihin Alh Haruna Uji da Wakokinsa"
Za'ayi Taron kamar haka:
Rana=Asabat 9th November 2013 Guri=Dakin Taro na sakandire fantai Hadejia Jigawa state Lokaci=10am
Baban Bako na musamman;
mai girma gwamnan jihar jigawa Alhaji Dr sule Lamido con.
Uban Taro;
Mai Martaba sarkin Hadejia Alhaji Adamu Abubakar Maje Con.
Shugabannin Taro;
1.Alhaji Suleman Baffa
2.Alh Muhammadu Daguro
Masu Masaukin baki:
1.Mai girma shugaban karamar hukumar Hadejia Alh Abba Haruna
2.mai girma dan majalissar jiha mai wakiltar Hadejia Alh Aminu Abus
3.Mai girma mai bawa gwamna shawara akan harkokin dalibai Alh Umaru Danjani.
Bako mai jawabi;
Mai girma kwamishinan Ilimi na jihar Jigawa Farfesa Haruna Wakili.
Mai bitar Littafi;
Shugaban kwalejin Ilimi ta jihar Jigawa Dr. Dahiru Abdulkadir.
Babban mai kaddamarwa;
Pharm.Hashim Ubale Yusufu
Mataimakan masu kaddamarwa
1.Mai Girma shugaban jam'iyar PDP ta jihar Jigawa Alh Salisu Mamuda.
2.Mai Girma kakakin majalissar dokokin jihar jigawa Alh Adamu Ahmed
sarawa.
3.Mai Girma mataimakin kakakin majalissar dokoki Abdu Alh Dauda Karkarna.
4.Masu Girma Ciyamomin Hadejia da Auyo da k/Hausa da Kaugama da m/madori da Guri da birniwa daKirikasamma.
5.Masu Girma yan majalissar Hadejia, Auyo. K/hausa, Kaugama, M/madori da Guri da Birniwa da Kirikasamma
6.Mai Girma kwamishinan matasa da raya al'adun gargajiya Alh Babandi Muhammad.
7.Alhaji Salisu Sambajo MFR
Masu Rera Waka;
1.Alh Aminu Ladan Ala
2.Fati Niger
3.Saddiq zazzabi
4.Surajo mai Asharalle
5.Dan Kwamarado
Masu Gabatar da Taro
1.Alh Baffa Bura FNICPR
2.Alh Umar Kiyari Jitau Madamuwa
3.Salmanu Adamu Rishi.
Allah ya bada ikon Zuwa.
Tuesday, October 22, 2013
KA SAN KANKA DA KANKA! (TAMBAYOYI 50) DAGA HARUNA AMINU HARUNA.
Muna cikin wani zamani, da mutane, sunfi damuwa da bayani akan wasu fiye da kansu, sunfi binciko laifin wasu fiye da nasu
Sayyadina Umar yace kuyi wa kanku hisabi kafin ayi muku, Abubawanda suke jawo tsira, Bautawa Allah shi kadai da Iklasi, akan sunnar Manzon Allah, a cikin Akida, da Ibada, Da mu'amalah, da Halaye masu kyau, yiwa kanka tambaya, hamsin don kasan matsayinka :
Allah yasa mu dace :
1- waye ya yika ?
2- mai yasa ya yika ?
3- kai waye ?
4- A ina kake ?
5- mai kake yi ?
6- Ina zaka ?
7- mai zai faru ?
8- mai kafi so a rayuwarka ?
9- mai kafi ki rayuwarka?
10- Duk abinda kakeyi, kana da hujja a sharia?
11- su waye abokanka?
12- Yaya zamanka da iyayanka?
13- Yaya zamanka yake da iyalanka?
14- Wace kungiya kakeyi don me?
15- A kwai wani yanzu haka da bakwa shiri da shi?
16- Tsakaninka da Allah ka taba cin amanar wani?
17 Kanayin karya?
18- Kana Dun guma ashariya?
19- Yaya zamanaka da makotanka?
20- Wace shedar ilmi kake dauke da ita?
21- kana salloli a Jam'i musamman a masallaci?
22- yaya alakar ka da danginka take ?
23- shin kana sada zumunta?
24- shin kana bayar da sadaka ?
25- shin kana karanta Alkur'ani mai girma?
26- kana azumin litinin da Alhamis?
27- kana sallar Shafi'i da wuturi?
28- kana zuwa asibiti domin ziyarar marasa lafiya?
29- Kana yawan saba alkawari ?
30shin kana azumtar kwanaki masu haske, ranar
sha uku, sha hudu, sha biyar?
31- shin kana kiyamul- laili?
32-kana umarni da kyakyawa da hani da mummuna?
33- kana zuwa aiki akan kari kuma ka tashi akan lokaci?
34- kana zuwa gaban malami domin daukar karatu?
35-ka tabbatar abinda kake ci halal ne?
36- kana kuwa damuwa da halin da yan uwanka musulmi suke ciki?
37- kana taimaka marayu kuwa?
38- salati nawa kake yiwa Annabi saw kullum?
39- Istigfari nawa kakeyi kullum?
40- kana zuwa makabarta domin tuna lahira?
41- kana zuwa taaziyya da sallar Jana'iza?
42- ka taba yin kuka saboda tsoran Allah?
43- shin kana yiwa dukkan musulmi sallama ko
kuwa sai wanda ka sani?
44- kanayin rantsuwa akan karya kuwa?
45- kana shan taba ko wiwi ko giya ko hodar iblis?
46- kana jin kade- kade, da wake- wake?
47- kana aske gemunka?
48- ka taba karbar cin hanci?
49- kana kyautawa iyalanka?
50- kana gaba da wani kuwa?
Allah yasa mu dace.
Wednesday, September 18, 2013
CIWON KODA A KASAR HADEJIA! DAGA PHARM. HASHIM UBALE YUSUF.
Bismillahir Rahmanir Rahim. Assalamu Alaikum.
CIWON KODA A KASAR HADEJIA: A bisa kididdiga, kimanin mutane miliyan talatin (30million) ne ke dauke da cutar Koda a tarayyar Nigeria. (National Association of Nephrology). Yawancin wadannan mutane na mutuwa kuwa katsam daga cutukan da suka shafi makwarar jini da zuciya, wanda ke da danganta da ciwon kodar. Wannan ya nuna cewa kimanin mutane ashirin bisa dari (20%) na ‘yan Nigeria na fama da wannan ciwo, wanda ana ganin alama daga yawan karuwar masu neman tace jini (dialysis). A wasu asibitocin zaka iske kimanin mutane 200 zuwa 300 ke zuwa neman tace jininsu a rana.
Cututtuka da dama na iya jawo ciwon Koda. Manyan dalilan dake hassada wannan ciwo anan karkarar sun hada da ciwo tsutsa (infections), kishirwa da kuma shaye shayen magunguna kai tsaye, Hawan Jini, shan taba da makamantansu.
Ita koda tana taimakawa jikine wajen tace dattin da kan taru a jikin mutum, sannan kuma tana taimakawa wajen tsotse ruwa, da sukari da sauran sinadaran gina jiki dake yawo a jini domin kar su bi fitsari su fice. Kenan zamu iya gani cewa idan har Koda bazata iya yin wannan tatar ba, to kuwa akwai matsala. Babban abun dazai faru kuwa shine, dattin na iya tare kofofin da jini da fitsari zasu bi, daga nan sai a fara kumbura, da kuma samun zazzafan ciwo na fitar hankali a hanyar da fitsari yake bi.
Sau tari zaka tarar mutane na aikin dake sa su zubad da gumi mai yawa, amma babu ruwa a kusa dasu. A kauyuka da rugage, zaka samu rijiyoyi sun kafe, ko kuma zasu sha ruwa gurbatacce, saboda ba inda zasu samu ruwan mai kyau su sha. Wannan bala’i ne.
Sannan kuma, yanzu wani abu wanda yake kamar gasa shine shaye shayen magunguna babu dalili ko kuma babu neman shawarar masana.
Wannan ka iyasa shan gurbatattun magunguna ko na jabu wadanda zasu iya cutar da ita kodar ta daina aiki. Haka kuma shaye shayen maganin gargajiya na daya daga cikin abubuwan da ke jawon wannan ciwo.
Akwai gazawar kayan aiki a asibitocinmu na tace jini da musayar koda, wanda hakan na jawo matsalar kai marasa lafiyar kasashen waje don warkarwa. A inda kuwa babu halin haka, sai addua kenan.
Tuesday, September 17, 2013
MARIGAYI SARKIN DOGARAI DA SAURAN MARIGAYA...
A cikin wadanda suka rasa rayukansu a sanadiyyar Hatsarin Mota a Hanyar Kano, Mutum goma sha daya ne! A wannan hoto kuma akwai Sarkin Dogarai da Galadiman Dogarai da Madakin Dogarai da Wamban Dogarai da Makaman Dogarai da Magayakin Dogarai da Garkuwan Dogarai da Chiroman Lema da Shitu Dogari da
Manu Mai Hoto.
Ya Allah Muna Rokonka da sunayenka tsarkaka Allah ka Gafarta musu. Amin.
Hadejia A yau!
SARKIN DOGARAN HADEJIA
WAMBAN DOGARAI.
Galadiman Dogarai
Sunday, September 8, 2013
****TAURARINMU HADEJIAWA PART SIX(6)****
Hadejia A yau.. Daga Muhammad Idris.
A ci gaba da kawo muku Tarihin wadanda Suka baiwa Kasar Hadejia Gudunmawa, yau Mun Tabo kadan daga Tarihin Marigayi Shatiman Hadejia Alh. Hassan Abbas.
****SHATIMAN HADEJIA ALHAJI HASAN ABBAS*****
Marigayi Shatiman Hadejia yana daya daga cikin dattijan arewa,manya a jihar kano da jigawa.Ya fara aiki tun daga Native Authority(NA) daga nan ya koma tarayya.Ya rike mukamin karamin ministan fetur a zamanin IBB. Shatiman Hadejia mutum ne mai kishin kasa da rikon addini. Shi ne sanadin aikin mutane da yawa a kaduna kuma har ya rasu akwai mutane da dama a zaune a gidansa.
Shatima ne ya fara gina katafaren gida domin saukar bakin kunya a Hadejia. Shi ya dauki dawainiyar
gyaran masallacin juma'a na lokaci mai tsawo.
Ya dauki nauyin sayen likkafani ga mamata har tsawon rayuwarsa. Arzik insa ya amfani 'yan uwa da sauran jama'a matuka domin akwai wadanda ya dauki nauyin ba su albashi har ya koma ga Allah subhanahu wa ta'ala.Muna addu'a Allah subhanahu wa ta'ala ya ji kansa ya albarkanci zuriyarsa.
Daga Muhammad Idris.
Wednesday, August 28, 2013
DANGANTAKA TSAKANIN BIRNI DA KAUYUKAN KASAR HADEJIA. DAGA M. HUSAINI SHEHU..
Daga M. Hussaini Shehu
DANGANTAKAR BIRNI DA KAUYE
Dangantaka tsakanin birni da kauye a kasarmu ta Hadejia tanada tsohon tarishi. Yana da wuyar gaske kasami bahadeje ko bahadejiya dake birni ko kauye da bashi da gidan yan’uwa ko gonar gado a daya daga wadannan wurare dana ambata.DA
Bukukuwan sallah-: shekarun baya zakaga kowane gida cike da baki yan’uwanmu na kauye sunzo cikin Hadejia domin sada zumunci da juna da kuma kallon buku kuwan sallah.
Wannan al’ada tamu tataimaka wa kasarmu sosai wajen jaddada hadinkai a tsakaninmu , kuma tataimaka wajen kawarda kyama tsakanin junanmu. Yanzu a wannan zamani irin wannan kyakkawar al’ada tamu tazama tarishi, sai ayi bukukuwan sallah a
gama bazakaga kowa a gidajenmuba. Kai koda wakilan kananan hukumominmu dawuya kasami guda uku daga cikin takwas sunzo domin sada zumunci kamar yadda akeyi a shekarun baya.
Kuma abin mamaki saika iske sauran masarautu bahaka sukeba, zakaga kowane shugaban karamar hukuma yazo sun hallara domin tattauna matsalolin wannan masarauta.
Shin minene yajawo
hakan? Nomi jide-: Inna tsammanin wannan al’ada tamu itace tasa ake cemana “Hadejia tsintsiya madaurinki daya”. Watau dadama daga cikin mutanan dake cikin Birnin Hadejia a shekarun baya sunada gidajensu nagado dakuma gonaki a kauyuka, aduk lokacinda damina ta sauka sukan koma gidajensu dake kauyuka
domin yin noma. Bazasu dawo gariba sai bayan damina. Zan iya tunawa mahaifina wata shekara muna shira game da wannan dabia tamu, sai yace mini: aduk cikin lokonmu gidanmune kawai yake ragewa da mutane idan damina ta sauka. Sauran makwabta kowa yakan koma kauye dominyin noma.
Saboda haka yan’uwa tayaya idanba hudubar shedanba zamu banbanta mutumun birni da kauye? Amsata shine duk mutumin kauyen Hadejia Dan Garin Hadejia ne sannan kuma duk mutumin Birnin Hadejia dan kauyen Hadejiane.
Tambaya anan itace idan Maganar danayi a baya gaskiyace, shin akwai maana idan mukayi maganar rabuwar kawuna tsakanin mutumin kauye dana birni?
Ga-manda-: wannanma wata tsohuwar al’adace tamu ta Hadejiawa da take kara nuna mana karfin dangan taka tsakanin kauye da birni. Bayan al’adar Nomu jide wanda kamar yadda nafadi a baya take nufin zuwa kauyukanmu da damina donyin noma, idan mungirbe mu kwaso amfanin zuwa gidajenmu na birni. Ha’ilayau mutumin birni musamman ma Mata sukan je ziyarar yan’uwa kauyu kammu bayan an kawo amfanin gona gida.
Ayayinda zasu tafi sukanyi guzurin
kayan miya wanda baa fiya samunsu a karkaraba, sukuma ayayin da suka gama zayararsu, yan’uwanmu na kauye sukan basu
amfanin gona kamar su: gero, dawa, wake dadai sauransu domin yin guzuri. Inna tsammanin wannan alada tamu haryanzu tananan anayinta tsakaninmu, to kaga kuwa ashe idan akwai wadannan dagantaka to ashe gaba dayanmu Hadejiawa yan’uwan junane. Saboda haka miye dalilin rabe raben kawuna tsakanin kauye da birni?
Sarauta-: Kowa yasani Sarautarmu ta Hadejia dama ta sauran kasashen Hausa ana nada Mai sarauta watau hakimi ko dagaci daga cikin yayan sarakai dake cikin gari a turasu kauyukammu domin yin mulki. Sannan ayayin
da hakimi zai tare kasarsa yakan tafi da sauran yaransa wadanda zasu tayashi mulki yazuwa kauye. Kuma dadama daga cikinsu idan sukaje zasu auri mata acan daganan sunzama yan can kauyen.
Shiyasa duk wani mai sarauta ko yaran mai sarauta a kauye idan aka binciki tarishinsu zaka iske zuwa yayi tare da hakiminsa ko dagacinsa Watau mutumin birnin Hadejiane, musamman ma da ya kasance al’adarmu ta Hadejiawa ta banbanta data Kanawa maana duk wanda fada ta tura kauye domin wakilci to zai zauna ne dindindin watau babu canji. Shiyasa idan shekaru sukayi yawa bama iya gane cewar zuwa mukayi donyin sarauta ba a nan muke ba shekarun baya. To amma abin mamaki saika iske yaron hakimi ko dagaci yana korafin nuna banbanci tsakanin birni da kauye. Shin akwai ma'ana a wannan dabia?
Allah yasa mugane.












