"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Saturday, September 29, 2012

A SHORT HISTORY OF HADEJIA BY MUSA USMAN MUSTAPHA.

HADEJIA A YAU!According to S.J. Hogben,
Hadejia town was founded in The 15th
Century. The assertion draws some authority
from the manuscript of the Kano chronicles,
where it was stated that, during the reign of
Yakubu Abdullahi Barjo who ruled Kano
from 1452AD to 1463AD. The King of
Machina Algalfati went to Kano with his
three Brothers. Sarkin Kano Yakubu gave
Sarkin Machina Algalfati the right to rule
Gaya and so he became the ruler of the
town. While one of Algalfati's brother went
to Rano where Sarkin Rano appointed him
the ruler of Dal. The second Brother
proceeded to Zazzau, where Sarkin Zazzau
appointed him the ruler of Gayan, And the
third Brother went to Garun Gabas, where
Sarkin Gabas appointed him the Ruler of
HADEJIA.

And established the dynasty which
ruled the town until the outbreak of the
19th century Jihad.
On the basis of this assertion, the town was
said to have been established sometime in
the 15th century, but the tradition which the
assertion was based on, contained certain
short comings which made its authenticity
doubtful. In the first place throughout the
period of our field work, not a single person
mentioned this tradition. And secondly
neither the tradition of Hadejia nor that of
the places (Kano, Gaya, Rano, Dal, Zazzau and
Gayan) mentioned the tradition, connect
their origins with each other.


And finally the fact that one of Algalfati's
brothers was appointed the ruler of the
town in the 15th century did not in any way
indicate that the town was established at
the time. In fact, if any thing, the tradition
only showed that the town was established
earlier than this development because a
ruler can only be appointed to an existing
town not the other way round.


(MUSA
USMAN MUSTAPHA)HADEJIA A YAU!

Friday, September 28, 2012

MUTUWAR SARKIN HADEJIA BUHARI

HADEJIA A YAU!
Bayan Sarkin Hadejia Buhari ya Gama
yake yake kamar yakin Takoko, gamon
kafur da sauransu! Sai ya yanke
shawarar ya fadada Kasar Hadejia daga
Gabas. Kuma a lokacin babu wani Dansa
da ya taso wanda zai bashi wata
sarauta bubba. Dan haka ya Nada
kaninsa Sarkiyo a matsayin Chiroman
Hadejia a shekarar 1863. Da nufin ya
zama Magajinsa, saboda Dansa Umaru
shekarunsa Goma sha Takwas (18).
Buhari yayi Tunanin ya Masa sarauta mai
Girma a Kasar Hadejia, dan haka yayi
kokarin ya masa sarautar Sarkin Auyo,
bayanda ya Kashe Nalara sarkin Auyo
ba'a nada kowa ba! Dan haka yaso ya
nada Umaru a matsayin Sarkin Auyo.
Wato ya kasance ya gajeshi bayan ya
Mutu.
Da wannan kudiri da yake ransa, Buhari
yayi kokarin ya cinye Gogaram (Bedde)
da Yaki don ya Nada kaninsa Chiroma
Sarkiyo a matsayin Sarkin garin. Kuma
dukda yayi haka zuciyarsa daya, wasu
daga cikin 'yan-uwansa sai suka yi
kokarin su baza masa abinda ya tsara!
Dan haka wani daga ciki 'yan-uwan
Buhari sai ya fara yada jita-jita a
tsakanin fadawan Buhari cewa yana so
ne ya kaisu a kashe su don ya cimma
wata manufarsa, su kuma fadawa sai
suka ga Dangantakarsa da Buhari bazai
fadi karya ba sai suka yarda da
maganarsa.
Dan haka fadawa sai suka fara shawara
a junansu ba tare da Sarki Buhari ko
wani ya sani ba, don su yiwa Buhari
tawaye a gun yakin, kuma duk suka
amince da hakan. Bayan kwanaki sai
Buhari ya sanar da fadawa cewa zasuje
suci Gogaram da yaki, amma bai san an
warware masa shirinsa ba. Aka saka
rana Buhari ya jagoranci mayakan
Hadejia don su ci Gogaram da yaki,
sarkin Hadejia Buhari ya shiga Gogaram
ta kofar Garin yamma amma mayakan
Buhari kamar su Sarkin Arewa Tatagana
da Sarkin yaki Jaji da sauran fadawa sai
suka tsaya suka ki su bi Buhari, ko da
ganin Haka sai Buhari ya shiga garin
suka fara dauki ba dadi da Mayakan
Sarkin Gogaram DAN BABUJE. Har suka
sokeshi da Mashi, kuma sai suka fice
daga Garin suka koma Bedde ta yanzu.
Koda mayakan Hadejia suka ga an
raunata Buhari sai suka bisu da yaki,
bayan sun dawo sai suka taho da
Buhari zuwa Hadejia, inda suka yi Gadon
Kara suka Dora shi. Akan hanyarsu ta
dawowa Hadejia Buhari ya musu jawabi
kuma suka fahimci cewa Munafurci ne
akayi tsakaninsu da Buhari. Kuma yace
musu lalle In ya mutu su kaishi Hadejia
su binne shi, kuma Allah ya dauki ransa
a Madaci kusa da Hadejia. Bayan fadawa
sun fahimci 'yan-uwan Buhari ne suka
munafurceshi, sai suka yanke shawarar
cewa dukda Kankantar Dansa Umaru shi
zasu Nada A matsayin Sarkin Hadejia.
Kuma hakan akayi karkashin jagorancin
Tatagana da Jaji. In kazo kayi Gaisuwar
Mutuwar Buhari sai ka Juya kayi
Mubaya'a a gun Sabon Sarki wato
Umaru Dan Buhari. Hadejia A yau.

Thursday, September 27, 2012

MUTUWAR SARKIN HADEJIA BUHARI...

HADEJIA A YAU! Bayan Sarkin Hadejia Buhari ya Gama yake yake kamar yakin Takoko, gamon kafur da sauransu! Sai ya yanke shawarar ya fadada Kasar Hadejia daga Gabas. Kuma a lokacin babu wani Dansa da ya taso wanda zai bashi wata sarauta bubba. Dan haka ya Nada kaninsa Sarkiyo a matsayin Chiroman Hadejia a shekarar 1863. Da nufin ya zama Magajinsa, saboda Dansa Umaru shekarunsa Goma sha Takwas (18). Buhari yayi Tunanin ya Masa sarauta mai Girma a Kasar Hadejia, dan haka yayi kokarin ya masa sarautar Sarkin Auyo, bayanda ya Kashe Nalara sarkin Auyo ba'a nada kowa ba! Dan haka yaso ya nada Umaru a matsayin Sarkin Auyo. Wato ya kasance ya gajeshi bayan ya Mutu.

Da wannan kudiri da yake ransa, Buhari yayi kokarin ya cinye Gogaram (Bedde) da Yaki don ya Nada kaninsa Chiroma Sarkiyo a matsayin Sarkin garin. Kuma dukda yayi haka zuciyarsa daya, wasu daga cikin 'yan-uwansa sai suka yi kokarin su baza masa abinda ya tsara! Dan haka wani daga ciki 'yan-uwan Buhari sai ya fara yada jita-jita a tsakanin fadawan Buhari cewa yana so ne ya kaisu a kashe su don ya cimma wata manufarsa, su kuma fadawa sai suka ga Dangantakarsa da Buhari bazai fadi karya ba sai suka yarda da maganarsa.

Dan haka fadawa sai suka fara shawara a junansu ba tare da Sarki Buhari ko wani ya sani ba, don su yiwa Buhari tawaye a gun yakin, kuma duk suka amince da hakan. Bayan kwanaki sai Buhari ya sanar da fadawa cewa zasuje suci Gogaram da yaki, amma bai san an warware masa shirinsa ba. Aka saka rana Buhari ya jagoranci mayakan Hadejia don su ci Gogaram da yaki,

sarkin Hadejia Buhari ya shiga Gogaram ta kofar Garin yamma amma mayakan Buhari kamar su Sarkin Arewa Tatagana da Sarkin yaki Jaji da sauran fadawa sai suka tsaya suka ki su bi Buhari, ko da ganin Haka sai Buhari ya shiga garin suka fara dauki ba dadi da Mayakan Sarkin Gogaram DAN BABUJE. Har suka sokeshi da Mashi, kuma sai suka fice daga Garin suka koma Bedde ta yanzu. Koda mayakan Hadejia suka ga an raunata Buhari sai suka bisu da yaki, bayan sun dawo sai suka taho da Buhari zuwa Hadejia, inda suka yi Gadon Kara suka Dora shi. Akan hanyarsu ta dawowa Hadejia Buhari ya musu jawabi kuma suka fahimci cewa Munafurci ne akayi tsakaninsu da Buhari. Kuma yace musu lalle In ya mutu su kaishi Hadejia su binne shi, kuma Allah ya dauki ransa a Madaci kusa da Hadejia. Bayan fadawa sun fahimci 'yan-uwan Buhari ne suka munafurceshi, sai suka yanke shawarar cewa dukda Kankantar Dansa Umaru shi zasu Nada A matsayin Sarkin Hadejia. Kuma hakan akayi karkashin jagorancin Tatagana da Jaji. In kazo kayi Gaisuwar Mutuwar Buhari sai ka Juya kayi Mubaya'a a gun Sabon Sarki wato Umaru Dan Buhari. Hadejia A yau.

Wednesday, September 26, 2012

THE 19TH CENTURY JIHAD AND THE ESTABLISHMENT OF HADEJIA EMIRATE.

Hadejia A yau. In assessing the impact of the 19th century Jihadist movement in Hausa land, (a major development in the History of the region), scholars and students of History have agreed that the movement created a political community much larger than any that had existed in the region before then. The process involved the suppression of several sovereign politics that that have developed over several centuries in the area. There was no doubt that internal forces within Hausa land, such as the widening gap between the ruled and the rulers, as a result of the corrupt policies of the later, contributed to this transformation. It is also our belief that the Jihadists (as Intelligensia of the society) served as agents of the internal development that took place in Hausa land at the beginning of the 19th century. But one still needs to ask the question why and how did the Jihadist come to exert such an important historical influence?

The origin of the Fulani Jihadist is a subject that has given rise to many conroversies. One undisputed fact is that some centuries ago they occupied the region of Tekrur, Futa Toro,and Futa Jallon between the Senegal and Niger Rivers. Since then, it is believed that they have been moving Eastward through Massina and the Hausa states toward chad, Fombina and beyond At the time of their movement, an important political development was taking place in Bilad at Sudan, especially in Borno and Kano in the late 15th century, and early 16th century. The period of the Jihadist migration into the above areas is a period of radical political change associated with Mai Ali Ghaji (1470-1503) in Borno and Muhammed Rumfa (1463-1499) in Kano.

The new ideas generated as a result of their policies had brought together people of diverse (descent) linguistic and occupational groups under one umbrella.

(page one).

By Musa usman Mustapha.

Duk mai bukatar Littafin zai iya tuntubar Baba Ali Najo K.liman.

Sunday, September 23, 2012

HISTORY OF HADEJIA

HADEJIA HISTORY
Prior to the rise of the emirate Council in
Hadejia, the territory now known as Hadejia
Emirate or Kasar Hadejia, was made up of
seven separate and distinct kingdoms namely:
Garun Gabas, Auyo, Dawa, Fagi, Kazura,
Gatarwa and Hadejia. Unfortunately, these
kingdoms possessed neither historical
documents nor codified oral traditions which
could throw light on their histories. Our
knowledge of these Kingdoms therefore
remains obscure and scanty. Available oral
tradition tells us that the rulers of each of
these seven Gudiri States received their titles
from, and owed allegiance to the Mai of
Borno through the Galadima, whose seat was
at Nguru. Furthermore, the same tradition
tells us that Auyo and Garun Gabas were the
oldest of the seven Kingdoms. The kingdom
of Auyo together with Tashena and Shira of
Katagum emirate were said to be founded in
about 1400 A.D. by immigrants from
Baghirmi, while Hadejia and probably the rest
of the kingdoms were founded afterwards.
The founders and early settlers of all the
Kingdoms east of Kano, we are told, were
attracted to this area by its richness in terms
of grazing land, fertile landscape. and fishing
streams. Hadejia town, for instance, owed its
name and origin to a Kanuri hunter from
Machina, Hade, and his wife, Jiya, who, while
on hunting expedition, became attracted to
the area because of its rivers and other
natural endowments. Hade became the
founder of Hadejia and the first in a long line
of Hadejia Kings - thirty-two in all who ruled
the area before the nineteenth century jihad.
Unfortunately, the names of only three of
these kings have been preserved – Baude,
Musa and Abubakar (Gowers, 1921). The
town and the kingdom, and indeed later the
emirate, got their name when Hade and his
wife Jiya settled in the area, and the people in
the surrounding settlements started to
migrate to, or identify the area with, them. It
is said that the people often referred to the
settlement as Garin (town of) Hade and Jiya
and later merged the two names and simply
called it HADEJIYA, after the name of the man
and his wife. Be that as it may, what emerged
from the little we know is that Hadejia
together with the six other kingdoms in the
region were all at one time or the other
brought under the control of Borno Empire.
They constituted what the Bornoans called
the "Nguderi or "Gudiri' territories. They
remained under Borno's imperial control up
till the beginning of the Nineteenth Century
when the Fulani conquered them and
subsequently transformed them into what
became known as the Hadejia emirate.
The founders of the emirate were a group of
nomadic cattle herdsmen who were
descendants of one Hardo Abdure. They were
said to have come from Machina in western
Borno in search of grazing land; and by the
end of the 18th century a sufficient number
of them had settled in the area due to the
availability of rich pasture. Accordingly, owing
to the growing number of Fulani
communities in the area, Sarki Abubakar, the
last Hausa King of Hadejia, appointed one
Umaru B. Abdure as Sarkin Fulanin Hadejia in
about 1788.

Tuesday, July 17, 2012

KASAR HADEJIA DA KABILUN CIKINTA


HADEJIA A YAU! Kasar Hadejia tana da kabilu da dama wadanda kuma suke da yarensu daban-daban: kamar...
1, HAUSAWA
2, ABORAWA (FULANI)
3, MANGAWA
4, GIZMAWA
5, BADAWA
6, KOYAMAWA.

1, HAUSAWA:- Kabilar Hausawa sune kabila mafiya yawa a kasar Hadejia Domin su babu wadda zaice ga wani lokaci da suka shigo Kasar Hadejia, kuma tafi karfi a kasar sakamakon dadewar Garuruwansu. kamar Garun Gabas (Biram), Auyo, da Matsa. kuma ko zuwan Bayajidda Garun Gabas yazo ne ya samu Mutanen Garin suna yin yaren Hausa.

2, ABORAWA (Fulani):- Kabilar fulani sun shigo kasar Hadejia tun a Farkon karni na goma sha biyar (15) kuma sun shigo ne daga yankin Massina wasu kuma daga Katsina, kuma sun Taho ne daga Gabar Kogin SENEGAMBIA wato SENEGAL. Sun fara zama ne a Rinde wasu kuma sun Zauna a Jarmari wasu a Marke wasu a Adiyani da Margadu. Kuma ayarinsu ya kasu biyu Inda wasu suka wuce kasar Kano Karkashin Jagorancin Lamido Usman Kalinwama. A Karni na goma sha Tara (19) Wasu fulanin sun sake shigo Kasar Hadejia daga yankin Machina Karkashin Jagorancin Ardo Abdure Dan Jamdoyi. Kuma ance Kafin suzo Hadejia saida suka zauna a Kankiya ta Jihar Katsina. kuma wadannan fulani suke Sarautar Hadejia har zuwa Yau.

3, MANGAWA:- Kabilar Mangawa ko Barebari wadanda mafi yawancinsu suna zaune a Gabas da Hadejia da kuma Arewacin kasar Sun zo ne A karni na goma sha bakwai (17) sun taho ne daga yankin Borno kuma mafiya yawansu sun zo kasar Hadejia ne Tonon Azurfa da Tagullah. Inda kuma daga baya wasu sun shigo kasar Hadejia A lokacinda RaBe yaci Kukawa da Yaki sai suka kaura suka dawo kasar Hadejia, Kamar garuruwan Birniwa, Baramusa, Kacallari, da Sauransu.

4, GIZMAWA:- Gizmawa suma kamar Mangawa sun shigo ne a Karni na goma sha bakwai (17) kuma suma suna zaune ne a yankin Guri, Marma, Lafiya da sauransu kuma suma yarensu kusan kamar barbarci ne saidai wasu kalmomin da yake canzawa.

5, BADAWA:- Kabilar Badawa basu da yawa a kasar Hadejia, kuma suna zaune ne a Garuruwan Iyakar Hadejia da Bedde, Kamar Gayin, Adiyani, Margadu,da Kadira. wasu sun zauna anan ne tun kafin yakin Gogaram. wasu kuma sunce dama anan suke tuntuni. ganin cewa suna iyaka ne da Kasar Bedde.

6; KOYAMAWA:- Kabilar koyamawa suma basu da yawa kuma Dangin Barebari ne, sai dai zanensu ya bambanta. kuma yarensu ma ba iri daya bane. Kuma suna cewa sun taho ne daga Gabas da Sudan. sannan suna zaune ne a Kasar Kafin Hausa, Bulangu, Yayari, koyamari da sauran garuruwan kasar Kafin hausa.

7; TIJJANAI:- Kabilar Tijjanai fulani ne dake zaune a Yelleman kuma Malamai ne masu bin Darikar Tijjaniyya. shi yasa ake ce musu Tijjanai. Sun shigo kasar Hadejia a shekarar 1903, Daga Malo a yankin Tukolar Senegal. sun taho ne bayan Turawan France sun yiwa Yankinsu Mulkin Mallaka. Sun taho karkashin jagorancin Shugabansu Muhammadu El-Bashir, kuma sun fara zama ne a Lokoja. Magajinsa kuma Ahmadu Madaniyyo sai ya sake tasowa daga Lokoja yazo Kasar Hadejia aka basu Wuri suka zauna. wato Yelleman Tijjanai. Alhamdu lillahi. Hadejia A Yau.

Sunday, July 15, 2012

TARIHIN ALH. DANJANI HADEJIA


HADEJIA A YAU! Tun Lokacinda nace zan rubuta tarihin Alh. Danjani Hadejia na samu kiraye kiraye a waya akan cewa ana sauraro na. To matsalar itace muna nan muna tattara Bayanai domin kar muyi garaje bamu kammala ba mu saki. Mai Karatu zaiga na rubuta Tarihin Alh. Danjani Hadejia, Wannan satin in Allah ya yarda zamu Maida Hankali wajen Tarihin Alh. Danjani Hadejia. Da irin gwagwarmaya da yayi. Alh. Danjani yana daya daga cikin Mutanen da suka Daga darajar masarautar Hadejia idan mukayi la'akari da irin gudunmawar da ya bayar wajen ganin Talaka yayi kyakkyawar rayuwa babu Tsangwama daga masu sarauta. Abinda yasa bazamu Rubuta duk tarihin ba sai mun samu Hotonsa wanda yayi da farar riga da bakin takalmi da kuma Jar hula. Hadejia a yau.

Monday, July 9, 2012

TARIHIN KAFUWAR HADEJIA KASHI NA (1)






TARIHIN KAFUWAR Hadejia Ya farune daga wani maharbi mai suna Hade, shi wannan maharbi ya taho ne daga yankin Machina ya yiwo yamma har yazo wannan wuri da yanzu ya zama Hadejia. Lokacin da yazo sai ya iske Daji mai bishiyoyi ga kuma Namun Daji da Tsuntsaye ta ko ina, sai ya zauna yaci gaba da farautarsa har saida wata rana yana tafe da karyar sa sai tayi nisan kiwo ko da tazo sai yaga duk jikinta da ruwa, sai yayi mamakin hakan har ma sai yabi sawunta. Koda yaje sai yaga kogi kuma ga tsuntsaye suna shawagi a wurin. Sai ya yanke shawarar zama a wannan wurin, kuma hakan yayi. Anan ya zauna yayi bukkarsa yake harbe harben Namun daji kuma yayi SU,wato kamun kifi. 

In ya kashe namun daji sai yaje ya sayar da fatun. Harma ya dauko matarsa wato Jia ya dawo da ita wannan wurin. Kuma mutane sai suke zuwa sayen fatu da nama a wurinsa. Duk wanda yazo wurin sai yayi sha'awar zama a wurin, haka nan gari ya fara bunkasa wasu maharba, wasu masinta, wasu kuma mafarauta. Sai gari ya kafu kowa yazo wucewa sai ya yada zango a garin. Kuma makwafta masu zuwa sayen Namun Daji sai suke kiran garin da suna Garin Haden-jia, wato suna masa lakabi da sunan matarsa. 

To kasancewar gari sai da shugabanci ne yasa shi Hade ya zama shugaban garin, duk wanda zaije sayen fatu ko nama sai yace na tafi garin Haden jia.
Wato ana masa lakabi da sunan matarsa. To sakamakon takaita kalma irin ta Bahaushe sai aka dunkule sunan ake cewa Hadejia.

Kuma bayan zamanin wannan mutumin
Hadejia taci gaba da zama gari kuma tare da shugabanci wato mulkin Sarakunan Habawa. Kuma a lokacin akwai kananan Garuruwa masu wadda suke kusa da Hadejia kamar Rubban Dakata, Auyo, Hadagwaigwai da dai sauransu. Wadanda suma suna da nasu sarakunan a wannan Lokacin. Kuma Hadejia sunyi Sarakunan Habe guda talatin da biyu(32),amma sunan mutum uku ake dasu wadanda sukayi mulki kafin zuwan Fulani. 
1, BAUDE 
2,MUSA 
3, ABUBAKAR. 

A zamanin Mulkin Sarkin Hadejia na Habe Abubakar fulani sukazo kasar Hadejia, kuma shine ya basu masauki a Hadejia Lokacin Hadejia tana karkashin Daular Borno, domin tana karbar Umarni ne daga Galadiman Borno. Sarkin Hadejia na Habe shi ya nada Umaru a matsayin Sarkin fulanin Hadejia. Wato kafin Jihadin Shehu usman Danfodiyo. Kuma har yanzu fulanin sune suke sarautar Kasar Hadejia.

A GABA ZAN KAWO MUKU TARIHIN
SARAKUNAN FULANI DA DALILIN KARBAR TUTA DA YADDA SUKA TUNKUDE SARAKUNAN HABE DAGA SARAUTA.

THE ORIGIN OF FULANI (Asalin Fulani)


Who Are the Fulani People? Origins The history of the Fulani seems to begin with the Berber people of North Africa around the 8th or 11th century AD. As the Berbers migrated down from North Africa and mixed with the peoples in the Senegal region of West Africa the Fulani people came into existence. Over a thousand year period from AD 900 - 1900, they spread out over most of West Africa and even into some areas of Central Africa. Some groups of Fulani have been found as far as the western borders of Ethiopia. As they migrated eastward they came into contact with different African tribes. As they encountered these other peoples, they conquered the less powerful tribes. Along the way many Fulani completely or partially abandoned their traditional nomadic life in favor of a sedentary existence in towns or on farms among the conquered peoples.

The nomadic Fulani continued eastward in search of the best grazing land for their cattle. Their lives revolved around and were dedicated to their herds. The more cattle a man owned, the more respect he was given.
Today, some estimate as many as 18 million Fulani people stretch across the countries of West Africa. They remain to be the largest group of nomadic people in the world. What Do the Fulani Believe? Religion and Beliefs:

The Fulani were one of the first African tribes to convert to Islam and are today more than 99% Muslim. The devout Muslim Fulani have seen themselves as the propagators and preservers of the Islamic faith in West Africa from as early as the fourteenth century. Historically it was a Fulani chief named Usuman dan Fodio, along with nomadic Fulani herdsmen who were instrumental in facilitating the spread of Islam across West Africa through evangelism and conquest. At times they would wage "holy wars" or jihad in order to extend and purify Islam. As the Fulani migrated eastward they spread their Islamic beliefs. As they became more powerful and attained more wealth they began to be more aggressive with their religion. 

Their adoption of Islam increased their feeling of cultural and religious superiority to surrounding peoples, and that adoption became a major ethnic boundary marker. Some settled in towns and quickly became noted as outstanding Islamic clerics, joining the highest ranking Berbers and Arabs.

Sunday, July 8, 2012

WAKAR SAUDATU ADO BAYERO






1. Daren jiya ba na yau bane gun kwanan
yaro daban da bubba.

2. Bismillah zana shirya waka sarki Allah
kaban basira inyi wakar saude 'yar nikatau.

3. Ina dada godiya ga Allah sarki shi ya halicci saude.

4. Ga saude sarauniyar kano mai saukin kai ce da son mutane.

5. Ga mai fara'a da son mutane Bata gaji tsiya da tsangwama ba.

6. A kyauta ba kamar ki saude kanwar
sarkin kano na yanzu.

7. Kanwar Sarkin Bichi na yau Nasiru Ado dan uwan ki Saude. 

8. Ga mai haske kamar Azurfa Dadin suna kamar Tagullah.

9. Taurari ko suna da haske basu kai hasken farin wata ba.

10. Inda mata suna sarauta a kano sai mun nada ki saude.

11. A zaria sunyi Quen Amina muma a kano muna da saude.

12. A gabas na dangana da Borno ba
kyakkyawa kamarki saude.

13. A yamma najeni har Ilorin ni banga ba
wadda tayyi saude.

14. A nan kudu har zuwa Adamawa banga ba wadda tayi saude.

15. A arewa na dangana Nijar duka babu
Diyar da tayi saude.

16. Kai duk matan dake Kano nai jam'i duk ba kamar ki saude.

17. Hotonki ana comment akanshi na kirga Comment dubu a yanzu.

18. Ga allura cikin duhu sai mai zurfin
hankali ka tsinta.

19. Ga saude bakin zare a matoya sai mai
hankali ka tsinta.

20. Ni burina a duniya inga kina mulkin
kano sa'ade.

21. Allah ba yadda bai iya ba a zazzau shi ya bai Amina.

22. A Ingila ga Elizabeth nan Allah shi zaya baiwa Saude. 

23. Ansa giwa cikin zubo taci guda bakin
rabonta kelau.

24. Allah in yai nufi ga iko nai babu abinda
zai hana shi.

Friday, July 6, 2012

THE ESTABLISHMENT OF SOME OF THE OLD SETTLEMENTS IN HADEJIA EMIRATE


HADEJIA A YAU!
We are severely constrained in the producing a coherent, meaningful and definite pattern of the process of the evolution of Hadejia emirate due to the limitation by our main source-oral tradition. Most of the traditions collected hardly touch on the process of the evolution of Kasar Hadejia. But in spite of this difficulty, we intend to take a second look at the source through a new-interpretation in the hope of coming out with a better understanding of the process of the evolution of Hadejia emirate. Towards this end, we shall attempt to discuss the process of the evolution of certain Old settlement in the emirate, with a view to paving way towards grasping the process of the evolution of Kasar Hadejia as whole.

Prior to the jihadist conquest at the beginning of the 19th century, the territory now known as Hadejia emirate consisted of several separate and distinct Kingdoms whose rulers received titles from and owed allegiance to the Habe Galadima of Borno.

The former Habe Kingdoms included Auyo,Garin Gabas(Biram),Hadejia,Kazura,Gaturwa,Marma,Dawa and Fagi. The process of the evolution of these Kingdoms of seems to be obscure except perhaps for the Kingdoms of Hadejia,Auyo and Garin Gabas.

At the time of the foundation of Hadejia,a number of small settlements were said to have existed in the territory that came to be known as Hadejia emirate. For example,on the North-eastern side of Hadejia town, there was Madagwaigwai, whose present site is near Rubban Dakata a village about 10kilometres east of Hadejia Kiri kasamma road. While on the eastern side of the town was Maskangayu (kulunfardu), a village said to have been established by Damagarawa immigrants whose ancestors now live in Hadejia (ILALLAH).

The old site of Kulunfardu was located near Tandanu, just by the valley of River Hadejia, about 15kilometres from TURABU.

There was a tradition in Turabu which said that, at the side of kulunfardu, there was a large Tamarind (Tsamiyar linzamai) whose branches were said to have bent due to the weight of the Luggage of soldiers of Mai Ali of Borno when they camped there on their way to attack Kano during the reign of Sarkin Kano Muhammadu Kambari Dan shariff(1731-1734) By the western side of Hade's camp was KADIME (still located to the site) which was about 9kilometre from Hadejia. By the Northern side of Hadejia was Majeri a few kilometre from Mallam madori, and by the southern side were Auyakayi(Tunawa), Unik(Arki), Majawa and Auyo.

These settlement were clearly established in the surrounding areas much earlier than Hadejia town.
End of page One.

A short History of Hadejia 1800-1906. By Musa Usman Mustapha.
Ana saida shi a k.liman.

Thursday, July 5, 2012

SARKIN HADEJIA BUHARI DA WAZIRIN SOKOTO A KATAGUM KASHI NA (2)

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU!

A kashi na farko kunji yanda Buhari suka kare da Wazirin sokoto da Mutanen Katagum: da kuma komawar sarki Buhari shabawa wato iyakar Hadejia da Gumel da kuma Damagaram.

YAKIN TAKOKO:- Bayan an Nada Ahmadu a matsayin Sarkin Hadejia, sauran Magoya bayan Buhari sai suma suka bar Hadejia suka koma Shafowa inda Buhari yake suka zauna tare. Sarkin Hadejia Buhari anan ya zauna tsakanin Takoko da Shafowa a Arewacin Hadejia da mutanensa kuma yake tafiyar da wannan yankin. Kuma iyakar Hadejia ce da Damagaram da Machina ta Arewa maso Gabas wato yankin Niger da kuma Borno. Kuma Buhari ya bada Gudun mawa sosai a wannan Yankin wajen Maidasu Musulmi. Inda yayi ta jihadinsa a yankin, kuma a wannan zama da yayi a Shafowa Buhari ya samu kyakkyawar dangantaka da Sarkin Machina da kuma Shehun Borno Umar wanda ya mulki Borno a wannan shekara (1835-1880) wannan dangantaka ta kara baiwa Buhari karfin gwiwa.


A shekarar 1851, Sarkin Musulmi Alu Bubba ya yanke shawarar daukan matakin Karshe akan Buhari, saboda yana tunanin Shehun Borno zaiyi amfani da Buhari ya rusa Daular Sokoto saboda ya zame musu Barazana a Arewa Maso Gabas. A wannan lokacin kuma DanGaladiman Sokoto ya hada Mayaka daga Hadejia,Kano,Katagum,Misau da Jama'are zuwa shafowa.

A wannan lokacin kuma Buhari ya fita kudu da shafowa shi da Sarkin Machina yana garin Takoko shida Jarumansa. A lokacinda Dangaladiman sokoto suka fito su yaki Buhari sai ya zabi Sarkin Jama'are Samboli ya jagoranci yakin, saboda shi ya fisu sanin Yankin. A ranar da zasu yaki buhari kuma a ranar Buhari ya shirya mamaye Garuruwanda suke kudu da Hadejia, sai aka hadu a Garin Takoko. Yayin da aka hadu aka gwabza fada Buhari yaci Galaba a kansu duk suka gudu, Sarkin Hadejia Ahmadu yayi kokarin ya Gudu Kasar Kano amma sai Barde Risku ya bishi ya Kashe shi.

Bayan Yakin Takoko yazo karshe kuma an kashe Sarkin Hadejia Ahmadu Amma ba'a son ran Buhari ba kuma aka masa Sallah aka kaishi Hadejia aka binne shi, sannan sai Buhari ya koma Hadejia yaci gaba da Mulki. Sakamakon wannan yakin, dangantaka ta sake baci tsakanin Hadejia da Sokoto, kuma Sarkin Musulmi yaki yarda da ya nada Buhari Sarkin Hadejia. Sai ya nada Tukur Na yayari, kanin Sarki Ahmadu kuma yace ya zauna a Mashama a Kasar Katagum a Matsayin sarkin Hadejia ya Gaji wansa Ahmadu. Amma Tukur bai yarda ya zama Sarkin Hadejia ba saboda yana tsoron Buhari, sai yaga bazai iya yin haka ba. Kuma saboda Gudun kar Buhari ya kasheshi sai Tukur ya Gudu daga Mashema yayi kaura zuwa Kano Lokacin Sarkin Kano Usman Na1(1846-1855) Sai aka Turashi ya Mulki Yayari a Kasar Birnin Kudu. (Yayarin Tukur) Tukur ya zauna acan Har zuwa lokacinda ya Mutu 1909. Buhari kuma yaci gaba da mulkin Hadejia yana kai hare hare a matsayin Jihadi Har saida yakai Gabasawa,Sankara,Ringim da Kuka kwance A Arewa maso yamma. A Kudu saida ya mamaye Kununu,Takalafiya, Kafin baka, Doma, Ruba, Itas da Kwanda. A Gabas kuwa saida ya Mamaye Babuwari, Kazura, Dawah, Gatare da Margadu. Saida Sarki Buhari ya fadada kasar Hadejia tafi Ko ina fadin Kasa a karni na19.

GAMON KAFUR:-

Tuesday, July 3, 2012

DAJIN DUHUN KARO A HADEJIA.



HADEJIA A YAU! 

DUHUN KARO:-duhun karo wani Daji ne dake kasar Hadejia kuma yafi yawa a Gabashin Hadejia. Wannan Daji daji ne mai Dimbin tarihi wadda duk wadda yake kasar Hadejia zaice maka haka ya taso yaga wannan Dajin. Hasali ma wadda ya kafa Hadejia (HADE) ni'imar wannan Daji ce tasa ya zauna a wannan yanki. Dajin Duhun Karo yana tafe ne da Ruwa a Gefensa sannan ga Itatuwa masu bin Danshin ruwa a gefen ruwan, Kuma wannan dajin ya taso ne tun daga Falgore yamma da Kano har ya dangana da komadugu ta Jihar yobe, sannan ya nufi Jihar Borno har zuwa Tafkin Chadi.

Wannan Daji ya kasu da yawa a Kasar Hadejia inda ya bazu kuma yafi girma da Ni'ima a Yankin Baturiya da Gabta da yankin Kadira har ya shiga zuwa Kasar Gorgaram.   Duk wadda ya saba bin hanyar kano ta Ringim zai ga wannan dajin musamman kwanar Auyo zuwa Hadin mai dan karofi inda nan ne ya fito har bakin titi musamman ma Burtalin fulani na Wajedu, sannan shine ya shiga Muhimbira har fateka zuwa Bubbar Riga yayi Gabas har Sansanin Sarkin Damagaram Tanemu. 


Na shiga wannan Dajin kuma banda kukan tsuntsaye da Namun daji babu abinda kake ji. Nayi tafiyar kilo meter takai biyar a cikin dajin, har saida ya Kaini Askandun fulani da Akurya, na gamu da wani Bafulatani mai suna Musa kuma na tambayeshi shekarar sa nawa a wannan dajin? Sai yace shima anan aka haifeshi, kuma yanzu shima yana da 'ya'ya wadanda ya haifa a wannan Dajin. Na tambayeshi ko zai bani labarin wannan dajin? Sai yace ya tashi yaga Kuraye suna zuwa suna razana musu shanu, kuma yace akwai Namun daji kamar Gada, Barewa, Bauna da dai sauransu. Amma tunda aka fara sarewa dajin sai sukayi nisa kuma da 'yan farauta da suka damesu. Yace Amma har yanzu akwai kananan Namun daji kamar Zomo, Guza, kuma wani lokacin ana samun Gada. Tsuntsaye kuwa dukda harbi da ake Har yanzu akwaisu da dama.
Dajin in ka shiga cikinsa baza kasan ana rana ba saboda tsabar Inuwa da take ciki kuma ga Ruwa a gefensa. Akasarin bishiyoyin da ke dajin farar kaya ce da kuma Bishiyoyi kamar su Danya, Darbejiya, Gabaruwa, Kirya, Kanya, Magarya,  da sauran bishiyoyi masu Ni'ima.


Kalu balenda wannan Daji yake fuskanta shine Sare saren Bishiyoyi da ake yi a cikinsa da kuma fadada Gonakai da makwaftan dajin sukeyi. Ta wani fannin kuma akan samun wasu suna kunna masa wuta. Amma dukda haka in ka shiga zai baka sha'awa. Na tambayi wani dattijo mai suna Garba Tandanu mai shekara 60, yace wannan dajin yasan lokacin da kuraye suke Hanasu zuwa Hadejia ta Rugar Isa inda sai sun zagaya ta Tuwankalta sannan zasuzo Hadejia Amma yanzu sai dai tsuntsaye da kananan namun daji. HADEJIA A YAU.

Sunday, July 1, 2012

KASAR HADEJIA ZAMANIN SARKI ADAMU




HADEJIA A YAU! Hadejia tana daya daga cikin Garuruwan da ke Karkashin Tutar shehu Usman Danfodiyo! Jama'ar Hadejia Akasarinsu fulani ne da Hausawa da Mangawa. Kuma Suna bin Addinin Musulunci ne. Idan muka tabo Tarihin Hadejia tun lokacin mulkin Habe zamuga cewa dama ko a wancan lokacin Addinin Musulunci ne addinin mutanen Hadejia sai dai dan abinda ba'a rasa ba. Kafin a jaddada addinin Musulunci lokacin shehu dan fodiyo sarakunan Habe ne suke Sarautar Hadejia, kuma anyi sarakuna da dama kamar (1)Baude(2)Musa(3)Abubakar. Bayan Malam Sambo ya karbo tuta karkashin jagorancin Sarkin fulani Umaru sai Hadejia ta koma Karkashin mulkin Fulani.
HADEJIA A YAU! A yau Hadejia ta zama wata fuskar kasuwanci a jihar Jigawa, domin duk abinda ka sani na sayarwa zaka samu a wannan gari. A shekaru Hamsin baya In ba ranar Kasuwar Garin ba wani abin bazaka samu ba. Allah ya albarkaci Hadejia da kayan Lambu Irinsu Tumatir, Tattasai, Attaruhu, da sauransu. Wadannan ana yinsu ko wane lokaci a Hadejia ba sai da damana ba. Saboda Albarkar kogi da Allah ya bamu. Haka kuma fannin kayan Abinci kamar shinkafa,Alkama,Masara. Duk ba sai da damina akeyinsu ba a Hadejia. Saboda Albarkar da Allah ya bamu ta kasar Noma mai kyau. Idan muka koma batun Amfanin Abinda ke cikin Ruwa Hadejia A kullum Tana Fidda kifi kimanin Na Naira milyan Biyu a takaice! Wani abu da yake shine Kalu bale a garemu shine.........

Saturday, June 30, 2012

GWAMNATIN JAR HULA. SAI KANO


HADEJIA A YAU! Tarihi shike maimaita kansa! Kamar yanda aka sani a da can mun san wasu dattijai wadanda kullum Adonsu shine: farar riga bakin takalmi da Jar hula. Bamu sani ba ashe adon nasu yana da fa'ida, ba wai suna yi bane dan kansu. A lokacin jamhuriya ta daya anyi jam'iyyun siyasa da dama a cikinsu har da NEPU. Kuma kowace jam'iyya tana da nata taken kuma tana da Tuta Irin tata. To ashe wannan adon da mukaga wasu daga cikin Dattijanmu sunayi ado ne mai ma'ana saboda suna cikin jam'iyyar NEPU. Kuma sun saka akidarta a ransu shi yasa suka maida adonsu irin na tutar jam'iyyarsu. Haka ma a jamhuriya ta biyu anyi jam'iyyu da dama a ciki harda P.R.P. Kuma su 'yan jam'iyyar NEPU sune suka kafa P.R.P. Dan haka sai suka sake saka alamarsu ta da can ta zama itace dai alamar P.R.P.
KWANKWASIYYA!
A shekarar 2011 Kano ta sake maimaita wannan tarihi karkashin Gwamna Rabiu Musa Kwankwaso Inda ya dawo da wancan adon na 'Yan NEPU. Shima ya maida adonsa farar riga da Jar hula kuma hakan ya samu karbuwa ga jama'ar kano. Yanzu farin yadi da jar hula kasuwarsu tafi garawa ba wai kano kadai ba harda jigawa da Bauchi da Kaduna da Katsina. Sai dai da yawa masu saka Jar hula in ka tambayesu basu san Ma'anar Hakanba. Kawai dai sunga Kwankwaso yana sakawa.

Wednesday, June 27, 2012

KANO GARIN ALHERI.


HADEJIA A YAU! Kano ba gari ba Dajin Allah Inji masu iya magana! Tarihin kano abu ne wanda sai dai ace an baka kadan daga cikinsa, domin tarihinta bazai kammalu ba ga duk mai rubuta shi. An kafa kano tun a farkon karni na biyar bayan haihuwar Annabi Isah (AS) wato 500AD. Idan akayi la'akari da zuwan Bagauda da mutanensa. Tun daga wannan lokacin ake mulkin kano kawo yanzu mulkin fulani.
Kano ta shahara ta fannoni daban daban kama daga Ilmin Addini da na boko da kuma Uwa uba kasuwanci wanda ta zama babu kamarta a duk jihar Arewa. Al'adunsu da dabi'unsu abin koyi ne ga duk wanda yayi mu'amala dasu. Allah ya albarkaci kano da Ni'imomi daban daban wadanda basu misaltuwa. Kasuwa kuwa duk abinda ka sani ana sayarwa a duniya zaka samu a Kano, kuma duk abinda kake sayarwa zaka samu masu saye.
Kano ta zama wata cibiya ce wanda duk abinda ya sameta lalle ya samu duk jihar Arewa baki daya. A watannin baya ne kano ta samu kanta a wani hali wanda bata taba zatonsa ba. Wato na hare haren bom da kashe kashen jama'a wanda hakan ya kawo cikas a al'amuran yau da kullum. Amma duk da haka ba'a fasa saye ana sayarwa ba kamar yanda aka saba. Lalle duk abinda ya taba hanci to idanu zaiyi ruwa! Wato duk abinda ya taba kano to hakika ya taba Arewacin Nigeria.
Jama'ar kano da ma Arewacin Nigeria... Na rigingine fa ba-a fada masa ganin farin wata. Ina nufin mun san gurin wanda zamu kai kukan mu, shine sarkin da ya kafa kano ya albarkaceta da mutane Irin su WAZIRIN KANO, Da sauransu. Muna rokon Allah ya karemu daga duk abinda zai kawo barazana ga Kano da ma Arewacin Nigeria. Allah ka mana maganin abinda yafi karfinmu da abinda bamu zaton sa. Domin da ikonsa ne komai ya kasance da kuma abinda zai kasance. KANO KWARYAR KIRA MATATTARAR ALKAIRI. Daukar Nauyi freedom Radio kano.

Tuesday, June 26, 2012

RABE DA MUTANEN BORNO


HADEJIA A YAU!
Baramusa wani kauye ne a karamar hukumar Birniwa! Naje ziyara kauyen kuma ganin cewa duk barebari ne a garin, sai na samu damar in tambayi tarihin Rabe dan Fataralle. Na samu wani dattijo mai shekara 76, sai na tambayeshi tarihin Rabe. Kafin ya bani amsa saida ya tsinewa Rabe.
Yace wani mutumin sudan ne wanda ya Addabi bare bari tun daga kukawa Har zuwa Bedde. Sannan yace Rabe ne dalilin zuwansu nan kuma yace duk Babarbare ko bamangenda naganshi a Kasar Hadejia ko wani Guri, to lokacin Rabe ne suka Gudo nan. Yace kamar Kacallari,Kaigamari,kuka Ingiwa,Birniwa.kirikasamma,Jibori, da sauransu duk Gudun Rabe sukayi. A lokacinda Rabe yaje kukawa ya kashe duk mutanen Garin wasu da suka samu labari sai sukayi gudun hijira kasar Hadejia. Wasu kuma suka shigo cikin Hadejia kamar Gagulmari,Kakaburi,zonagalari,kilabakori da sauransu. Yace da can suna da zanen barebari amma yanzu sun canza sai suke zanen a kan fuskarsu wato uku uku. Sauran Labarin sai a Gaba.

Monday, June 25, 2012

GARKO DA SANA'AR SU. TUN KAFIN ZUWAN BATURE


HADEJIA A YAU! GARKKO Unguwar Garko Tana daya daga cikin unguwannin da suke Garin Hadejia, kuma Unguwa ce mai dimbin tarihi idan mukayi La'akari da Dadewarta. Garko tana daya daga cikin garuruwanda sarakunan Habe suka mulka a Hadejia amma A lokacin Gari ne mai zaman kansa kafin ya hade da Hadejia ya zama Unguwa. Kuma suna da sana'ar su wanda suka gada Iyaye da kakanni. Hakan ta bunkasa tattalin Arzikinsu tun a wancan lokacin zuwa yanzu. Sana'ar su Itace Amfani da kasa ko yumbu domin yin Randa,Gajirami,Tukunya,Tuli,Kula,Kasko,kafara da dai sauransu. Kuma wadannan kayan sune kayan da ake amfani dasu a kasar Hausa kafin zuwan Turawa. Domin Amfanin Gida wato Girki ko Aje ruwa ko makamantansu. Na samu wani Dattijo yana gina Randa a kofar gidansa Na tambayeshi ko A ina suke samun yumbun da suke gina randa? Yace duk a Hadejia suke samu akwai Mailolo ta Gabas da Hadejia anan suke samo yumbun da suke gina duk abinda nagani anan. Na tambayeshi ko shekara nawa yana yin wannan sana'a? Sai yace ya kai shekara Hamsin da biyu yana yi, kuma suna yi ne da Mahaifinsa da kannensa har zuwa yanzu ya zamanto shine bubba. Na tambayeshi menene dalilin da in an gina ake zuwa a gasa ta a wuta? Zan kawo muku karashen firar mu.

Saturday, June 23, 2012

JUMA'A RANAR ALKAIRI


Ranar jumaa itace mafi alherin dukkan wata
rana da rana ta fito a cikinta. cikinta Allah ya
halicci Adam, cikinta ne qiyama zata tsayu,
kuma ita ranar idi ice ga musulmai.Don haka
nema aka sharanta wasu abubuwa acikinta,
daga ciki akwai: hudubar jumaa, wanka,
fesa tirare, fita cikinta da mafi kyawun kaya
da yanayi me kyau, yin kabarbari lokacin fita
sallar, kusantar liman, da kuma tara tunani
gaba daya domin sauraren wa'azi da
ambato (wato huduba).

Friday, June 22, 2012

TARIHIN RAYUWAR SHEIKH JA'AFAR M. ADAM


An haifi marigayi Sheikh
Ja'afar Mahmoud Adam a
garin Daura, a shekara ta 1962
(ko da yake wani lokacin
yakan ce 1964).
Marigayi Sheikh Ja'afar ya fara
karatunsa na allo a gidansu, a
wurin mijin yayarsa, Malam
Haruna, wanda kuma dan
uwansu ne na jini. Daga nan
kuma sai aka mayar da shi
wajen wani Malam Umaru a
wani gari wai shi Koza,
kimanin kilomita 9 a arewa da
Daura, wanda shi ma akwai
dangantaka ta jini a tsakanin
su, wanda kuma shi ne
musabbabin zuwansa Kano.
Bayan sun zo Kano ne tare da
wannan malami nasa, a
shekara ta 1971 (ko 1972), sai
suka zauna a makarantar
Malam Abdullahi, wanda
asalinsa mutumin jamhuriyar
Nijar ne, amma yake zaune a
unguwar Fagge a Kano. Tun
kafin zuwansu Kano, tuni
marigayi Sheikh Ja'afar ya riga
ya fara haddar Alkur'ani mai
girma, wanda ya kammala a
shekara ta 1978.
Bayan da Malam ya kammala
haddar Alkur'ani mai girma,
kasancewarsa mai sha'awar
ilimi, sai ya shiga makarantu
biyu a lokaci daya a shekara
ta 1980. Ya shiga makarantar
koyon Larabci ta mutanen
kasar Misra a cibiyar yada
al'adun kasar Misra, (Egyptian
Cultural Centre), sannan
kuma ya shiga makarantar
manya da ba su yi boko ba ta
Masallaci Adult Evening
Classes, tunda a lokacin
shekarunsa sun wuce shekaru
na primary, amma duk da
haka a wannan lokaci shi ne
mafi kankanta a ajinsu. Haka
ya rika yin wannan karatu
guda biyu: Waccan
makarantar ya je ta da
daddare bayan sallar isha'i,
waccan kuma ta koyo harshen
larabcin da yamma. Ya
kammala wadannan
makarantu a shekara ta 1983.
Wannan kuma shi ya ba shi
damar shiga makarantar
GATC Gwale a shekara ta
1984, kuma ya kammala a
shekara ta 1988. A shekara ta
1989, malam ya sami gurbin
karatu a jami'ar musulunci ta
Madinah, a inda ya karanta
ilimin tafsiri da Ulumul Kur'an,
wanda kuma ya kammala a
shekara ta 1993. Sannan kuma
Sheikh Ja’afar ya sami damar
kammala karatunsa na digiri
na biyu (Masters) a Jami’ar
Musulunci, A Oundurman Sudan.
Sannan kuma, kafin
rasuwarsa, ya riga ya yi nisa
wajen karatunsa na digiri na
uku, wato digiri da digirgir
(PhD), a Jami’ar Usman Dan
Fodiyo da take Sokoto.
Daga cikin malamansa na
ilimi, akwai malaminsa na
farko, mutumin kasar Masar,
Sheikh Abdul-Aziz Ali al-
Mustafa, da kuma Malam
Nuhu a unguwar Dandago,
wanda malam ya karanci ilimi
fikihun malikiyya da wadansu
littattafai na hadisi a gurinsa,
da kuma Malam Muhammad
Shehu, mutumin Lokoja,
wanda Malam ya karanci
nahawu da sarfu da balaga da
adab a wajensa. Akwai kuma
Sheikh Abubakar Jibrin
limamin masallacin Juma'a na
BUK, akwai kuma Dr. Ahmad
Muhammad Ibrahim shi ma na
jami'ar Bayero ta Kano. Daga
cikin malamansa na jami'a
kuma, akwai Sheikh
Abdurrafi'u da Dr. Khalid
Assabt.
Daga cikin karatuttukan da
malam ya karantar da su, sun
hada da tafsirin Alkur'ani mai
girma, Kitabuttauhiid,
Umdatul Ahkaam, Arba'una
Hadiith, Kashfusshubuhaat,
Bulugul Maraam,
Riyaadussalihiin, Siiratun
Nabawiy, Ahkaamul Janaa'iz,
Siffatus Salaatun Nabiiy.
Wasu daga cikin daliban
malam sun hada da Malam
Rabi'u Umar R/Lemo da
Malam Sani Abdullahi
Alhamidi Dorayi da Malam
Abdullah Usman G/Kaya da
Malam Usman Sani Haruna da
Malam Ibrahim Abdullahi Sani
da Malam Ali Yunus
Muhammad da Dr. Salisu
Shehu da Malam Shehu
Hamisu Kura da Malam Anas
Muhammad Madabo.
Kafin rasuwarsa, malam ya
fara gagarumin aikin rubuce
tafsirinsa a harshen Hausa a
karkashin wannan cibiya
(Sheikh Ja'afar Islamic
Documentation Centre).
Marigayi Sheikh Ja'afar
Mahmoud Adam ya rasu ranar
juma'a 26/Rabii'u Awwal/1428
(13/04/2007) sakamakon harin
da wadansu 'yan ta'adda suka
kai masa, a daidai lokacin da
yake jagorantar sallar asuba a
masallacin Juma'a na Dorayi.
Ya rasu ya bar mata biyu, da
'yaya shida, yayin da aka haifa
masa ta bakwai kwanaki 58
daidai bayan aiwatar da
wannan kisan gilla a kansa.
Dubun-dubatar mutane ne
daga ko'ina cikin kasar nan
suka halarci jana'izarsa, kuma
an binne shi ne a makabartar
Dorayi. Allah ya ji kan sa ya
gafarta masa, ya saka masa
da gidan aljanna. Amin

Thursday, June 21, 2012

SAKO ZUWA GA MASU AMFANI DA FACEBOOK


Malam Yusuf Audi, ya
rubuta cewa kamar haka...
Shafukan INTERNET da
Wayar hannu ta
GSM...... Bincike ya nuna
cewa shafin internet na
FACEBOOK da wayar hannu
ta GSM suna
daga cikin ababen dake
kara rura wutar
fadan addini a Nigeria.
Hakan yana faruwa
sakamakon irin yadda
mutane ke amfani da su
wajen isar da
sako atsakanin su.
Mutanen mu suna da son
bayar da labari,
ingantacce ko mara
inganci don neman
addu'ar 'yan uwansu ko
don nuna bajintar
su ko kuma don wata
manufa ta su ta
daban. Wannan yasa
dayawa sukan fidi abin da
ba
su da tabbas akan shi, ko
kuma suyi kari
cikin labarin na su. Ya kai
dan uwana me son bayar
da labari!
Kaji tsoron Allah, kada
kafadi, kada
karubuta sai abin da kaji
ko kagani ko
kuma kake da tabbas akan
shi. kasani za ka amsa
tamyar Allah akan abin
da kake fadi ko kuma kake
rubutawa
duniya(facebook), wacce
amsa katanada?
Ba wani abin birgewa
bane afara jin
labarin dake tayar da
hankali agurinka. Na ji
ance sun ce, wannan ba
dalili bane.
Addinin muslunci ya hore
mu da yin
magana ba tare da ILIMI
ba. Mu kiyaye ko Allah
(S.W.A) ya kiyaye mu. Ya
Allah! Kakiyaye mu,
kabamu zaman
lafia, amin.
To Jama'a sai mu kula da
fadar jita jita, domin karya
haramun ce. Allah ya kare
mu ameeeeeeeeen

Wednesday, June 20, 2012

KADUNA BA LAFIYA


HADEJIA A YAU! Rahotanni daga jihar Kaduna ya nuna cewa Har yau rikici bai lafa ba dukda Dokar hana zirga zirga da aka sanya a Jihar. Ko a yammacin yau anji Karar harbe harbe da kone kone a yankin Badarawa,Unguwar yero da kuma wasu sassa a Unguwar Dosa. Wani ma'aikacin Gidan Redio ya ruwaito cewa An harbi wani yaro a Gabansa, Bayan an kaishi asibiti daga bisani ya cika. Allah ya mana maganin wannan masifa! Kwanaki hudu dai kelau ana zaman Dar dar a Jihar Kaduna Rikicinda ya rikide ya zama na kabilanci da Addini.

HADEJIA A YAU! A Ranar Laraba In Allah ya yarda zamu kawo muku Tarihin masallacin juma'ar Hadejia da yanda aka kafashi. daga bakin M.Mu'azu Hamza. zakuji a shekarar da aka kafashi da kuma lokacin wane sarki ne? kuma shekararsa nawa zuwa yau? Limamai nawa ne suka jagorance shi zuwa yau? A wane lokaci aka maidashi na siminti? da sauran abubuwan da ya kamata mu sani. Hadejia A yau.

Tuesday, June 19, 2012

KOFOFIN HADEJIA



HADEJIA A YAU! Wadannan Hoton kofar Gabas ne da Kofar Kudu. An Gina wadannan kofofi ne Tun kafuwar Hadejia kuma haka nan akayi ta gyaransu har zuwa yau. sai dai kash! sakamakon Biris da halin ko in kula ya jefa wadannan kofofi a cikin tsaka mai wuya. kamar kofar Gabas wani yanki daga cikinta tuni ya rushe. Haka Kofar kudu wato Cediyar kyalesu in kaje wucewa idan ba kula kayi ba bazaka san akwai kofa a gurinba. muna kira Ga Karamar hukumar Hadejia da Masarautar Hadejia da a taimaka a gyara wadannan kofofi kamar sauran kofofi 'yan-uwansu. Ganin cewa ba dan ana gyaransu ba da basu kawo yanzu ba. kuma muna kira ga Sarakunan kofofi da su rinka yiwa Karamar Hukuma tuni akai akai domin a gyara wadannan kofofin. Allah ya Daukaka Masarautar Hadejia. Hadejia A yau.

HADEJIA A YAU! An sake sanya dokar awa Ashirin da hudu a Jihar Kaduna Sakamakon Tashin hankalin da ya biyo bayan harin bom din da aka kai a Zariya da kaduna. An samu labarin Jiya da dadare matasa sunyi ta kai farmaki a junansu da niyyar daukan fansa. Haka kuma yau ma fada ya barke a Unguwanni daban daban a kaduna. Dukda dokar hana zirga zirga da Gwamnan jihar ya saka. A Damaturu ma ta jihar Yobe rikicin ya lafa kuma suma ansa dokar Hana zirga zirga. Mutanen garin dai sun bayyana wannan abin a matsayin Gazawar Gwamnatin tarayya na kasa magance matsalar tsaro.

KOFAR KUDU DA KOFAR AREWA



HADEJIA A YAU! Kofar kudu da kofar Arewa.

Monday, June 18, 2012

TASHIN BOM A DAMATURU DAGA BBC HAUSA

Rahotanni daga Damaturu babban
birnin jihar Yobe dake Arewacin
Najeriya, sun ce mazauna unguwanni
da dama ne suka tsere daga gidajen
su, yayin da wasu karin suka
kauracewa unguwannin su domin
samun mafaka.
Wannan dai ya biyo bayan tashin
bama bamai da karar bindigogin da
aka rika ji ne ba kakkautawa a
yammacin yau.
Rundunar Hadin Gwiwar Samar da
tsaro a jihar Yoben ta tabbatar da
abkuwar lamarin, sai dai ba ta
bayyana adadin asarar rayuka da
jikkata da aka samu ba a sakamakon
wannan hari.
Harin na Yoben dai na zuwa ne
kwana daya bayan wasu hare haran
kunar bakin wake da aka kai kansu
coci-coci uku a garin Kaduna da
kuma Zaria.
Hare haran da kungiyar Ahlisunna
lidda'awati wal jihad da ake kira
Boko Haram suka yi ikirarin kaiwa.

HADEJIA A YAU! Sarkin Hadejia Sambo shine ya karbo Tutar Musulunci a gun Usman Dan fodiyo! Yayi mulkin Hadejia tun daga 1808 zuwa 1848. Allah ya masa Rasuwa a Mai-Rakumi. Kuma anan kabarinsa yake! A cikin 'ya'yansa akwai wadanda sukayi Sarautar Hadejia a lokacin yana Raye. Kamar Garko Gambo 1845t-1847, Abdulkadir Dan Sambo 1847-1848. Sannan Sambo yaci Gaba da Mulkin Hadejia kuma ya Rasu a wannan shekarar. Sai kuma Dansa Buhari Sai Ahmadu sannan Buhari Sai jikansa Umaru Dan Buhari. Sai kuma Dansa Haru Bubba. Allah ya Gafarta musu.

KABARIN SARKIN HADEJIA SAMBO


HADEJIA A YAU! Sarkin Hadejia Sambo shine ya karbo Tutar Musulunci a gun Usman Dan fodiyo! Yayi mulkin Hadejia tun daga 1808 zuwa 1848. Allah ya masa Rasuwa a Mai-Rakumi. Kuma anan kabarinsa yake! A cikin 'ya'yansa akwai wadanda sukayi Sarautar Hadejia a lokacin yana Raye. Kamar Garko Gambo 1845t-1847, Abdulkadir Dan Sambo 1847-1848. Sannan Sambo yaci Gaba da Mulkin Hadejia kuma ya Rasu a wannan shekarar. Sai kuma Dansa Buhari Sai Ahmadu sannan Buhari Sai jikansa Umaru Dan Buhari. Sai kuma Dansa Haru Bubba. Allah ya Gafarta musu.

MAI GORIBA


HADEJIA A YAU! Wannan Hoton Mai Goriba ne! Kusa da Maskangayu Inda Turawa suka fara kafa sansaninsu kafin su Shigo Hadejia. Bayan sunci Hadejia da yaki kuma sai suka gina Bariki Ta zama nan ne Gidajensu da Ofis dinsu Har zuwa lokacinda Nigeria ta samu 'yancin kai a shekarar 1960.

KOFAR MANDARA


HADEJIA A YAU! Wannan kofar Talata ce ko kofar Mandara! Tana daya daga cikin kofofin Garin Hadejia. Ta wannan kofar ce Turawa suka shigo Hadejia a 1906. Kuma da can babu ita Turawa ne Suka fasa Ganuwar Hadejia Suka shigo Shine Dalilin da ake ce mata Kofar Talata saboda Ranar Talata Turawa suka fasa ta suka shigo Hadejia ta cikinta. Hadejia A yau.

KOWA YA GYARA YA SANI


HADEJIA A YAU!
Assalamu Alaikum! Bayan gaisuwa da fatan
Alkairi Ga 'yan wannan Masarauta, Muna
kara godiya ga Allahu subhanahu-wata'ala
da ya bamu ikon Rubuta wannan wasika.
Domin da Ikonsa ne Komai ya kasance da
kuma abinda zai kasance! Bayan haka Ina
kira ga shugabannin Hadejia da su taimaka
su Inganta mana Muhimman guraren
Tarihinmu na kasar Hadejia. Sakamakon
Lalacewa da suke kokarin yi. Kamar Tsohon
Gidan yari, Gulbin Atafi da Ramin zaki, bariki
wato Gidan Rasdan da na D.O., kabarin
Captain H.H. Phillips wato Mai Tumbi, Kofar
Kudu (chediyar kyalesu) da kuma kofar
Gabas. Wani mutum yazo daga BIDDA ta
jihar Niger yace min Yana so na kaishi
Kabarin Captain phillips, sai nayi shiru Ina
tunanin wanene captain phillips? Sai na tuna
lokacin muna yara In munje kanya muna
zuwa kabarin Mai tumbi. Kuma a jikin
kabarin an rubuta captain H.H.phillips! Sai
nace masa Muje ko da mukaje sai na fara
Gabatar masa da Bariki cewa a nan Turawa
suka fara zama. Sai yace dani A'a ai sun
Zauna a can Gaba kafin suzo nan. Nace Eh
hakane. Koda mukaje Kabarin Mai tumbi sai
muka ga Ginin duk ya rushe kabarin yana
nema ya bata. Sannan sai yayi kira ga
Hukumomi su rinka kawata Guraren Tarihi
Irin wadannan. To muma muna kira ga
wadanda abin ya shafa da su Gyara guraren
tarihi ba sai kabarin Mai tumbi kawai ba.
Sannan yace In kaishi Fantai Inda Gidajen
Sarakunan Habe suke. Ko da yake munje
Amma bamu samu Dagacin Mandara a gida
ba amma mun Dauki Hotunan Gidajen nasu
da kuma Tsangayar Gwani Gambo a cikin
'Yankoli. Sannan Muka Zarce zuwa Mai-
Rakumi mukayi Ziyara ga kabarin Sarkin
Hadejia Sambo. Bayan mun dawo Mukayi
sallama da Bako ya wuce Gogaram Ta Bade
Yace daga nan Zaije har Ngazargamu. Nace
Allah ya kiyaye hanya. Sannan sai na fara
tunani Ashe tarihi yana da muhimmanci? Sai
na tuna Ai malamin History yace:- History is
the systematic Account of past and present
Event. Zan baku Karashen Labarin anan
Gaba. Hadejia A yau.

Sunday, June 17, 2012

JIYA BA YAU BA.



HADEJIA A YAU!
Assalamu Alaikum! Bayan gaisuwa da fatan Alkairi Ga 'yan wannan Masarauta, Muna kara godiya ga Allahu subhanahu-wata'ala da ya bamu ikon Rubuta wannan wasika. Domin da Ikonsa ne Komai ya kasance da kuma abinda zai kasance! Bayan haka Ina kira ga shugabannin Hadejia da su taimaka su Inganta mana Muhimman guraren Tarihinmu na kasar Hadejia. Sakamakon Lalacewa da suke kokarin yi. Kamar Tsohon Gidan yari, Gulbin Atafi da Ramin zaki, bariki wato Gidan Rasdan da na D.O., kabarin Captain H.H. Phillips wato Mai Tumbi, Kofar Kudu (chediyar kyalesu) da kuma kofar Gabas. Wani mutum yazo daga BIDDA ta jihar Niger yace min Yana so na kaishi Kabarin Captain phillips, sai nayi shiru Ina tunanin wanene captain phillips? Sai na tuna lokacin muna yara In munje kanya muna zuwa kabarin Mai tumbi. Kuma a jikin kabarin an rubuta captain H.H.phillips! Sai nace masa Muje ko da mukaje sai na fara Gabatar masa da Bariki cewa a nan Turawa suka fara zama. Sai yace dani A'a ai sun Zauna a can Gaba kafin suzo nan. Nace Eh hakane. Koda mukaje Kabarin Mai tumbi sai muka ga Ginin duk ya rushe kabarin yana nema ya bata. Sannan sai yayi kira ga Hukumomi su rinka kawata Guraren Tarihi Irin wadannan. To muma muna kira ga wadanda abin ya shafa da su Gyara guraren tarihi ba sai kabarin Mai tumbi kawai ba. Sannan yace In kaishi Fantai Inda Gidajen Sarakunan Habe suke. Ko da yake munje Amma bamu samu Dagacin Mandara a gida ba amma mun Dauki Hotunan Gidajen nasu da kuma Tsangayar Gwani Gambo a cikin 'Yankoli. Sannan Muka Zarce zuwa Mai-Rakumi mukayi Ziyara ga kabarin Sarkin Hadejia Sambo. Bayan mun dawo Mukayi sallama da Bako ya wuce Gogaram Ta Bade Yace daga nan Zaije har Ngazargamu. Nace Allah ya kiyaye hanya. Sannan sai na fara tunani Ashe tarihi yana da muhimmanci? Sai na tuna Ai malamin History yace:- History is the systematic Account of past and present Event. Zan baku Karashen Labarin anan Gaba. Hadejia A yau.

WASIKA DAGA AJI KIMA ZUWA GA SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR HADEJIA

Free Web Proxy
Budaddiyar wasika ga mai girma shugaban karamar shukumar Hadejia da yan majalissarsa.
Bayan gaisuwa irin ta addinin musulunci, ina mai farin
cikin rubutoma wannan takardar domin in nuna irin
goyan baya da nake bawa wannan jam'iya da wannan gwabnatin mai albarka, bayan haka ina jinjinama bisa irin kokarin da kake wajen ciyarwa da
wannan karamar hukuma gaba. Ina sake jinjinama da yadda kake gudanarwa da mulkinka cikin
kwanciyar hankali da zaman lafiya.
Bayan haka ina so nayi amfani da wannan damar na tunatar da kai wasu muhimman abubuwa
wanda idan kayi su zasu taimakama wajen samin sahihiyar
hanyar ci gaba da kuma adana tarihi ko bayan
ranka, wannan abun kuwa sune kamar haka.
Kasancewar garin hadejia babban gari ne mai tsohon tarihi a jeri garuruwan Hausa to ya kamata
ace yau akwai abubuwan da zamu yi alfari da su wajen tarihi kamar yadda ya'u idan kaje Daura zaka tarar da abubuwan da suka faru shekaru dari uku ko hudu
da suka shude kamar yau akayi su.
Ma'ana muma a garin Hadejia muna da irin guraren
nan kamar kabarin mai tumbi, kofar mandara, ruwan Atafi, Rijiyar turawa, mabuga, majema, marina, bariki da sauransu.
Kuma ya kamata ana tunawa da mutanan da suka bawa wannan gari gudunmawa misali saka
sunayensu a titinah,dakin taro makarantu dasauransu. mutane irinsu Alh Haruna uji ya kamata a
na tunawa dasu, amma abin al'ajabi aka saka sunayen mutane a titinah aka manta da Haruna
uji, wanda ya bada muhimmiyar gudunmawa wajen daukaka masarautar hadejia.
Saboda haka a madadin daliban Hadejia emirate ina
mika wannan sakon ga maigirnma shugaban karamar hukuma da fatan za'a duba. Nagode.
Comrade Aji kima hadejia secretary general Hadejia student Association.

Thursday, June 14, 2012

MANYAN BORNO SUN ROKI DA A KAWO KARSHEN RIKICIN BOKO HARAM

HADEJIA A YAU! Al'ummar Jihar Borno dake Arewacin Nigeria sun Roki 'yan kungiyar Jama'atu Ahlussunna lidda'awati wal jihad wadda aka fi sani da suna Boko Haram da su Amince a tattauna dasu da Gwamnati domin a kawo karshen Hare harenda yake janyo Rasa rayuka da gidaje. A wata fira da yayi da 'yan jarida a Maiduguri Dr. shettima Ali Munguno ya bayyana rikicin boko haram a matsayin rikici ne wanda ya janyo Asarar rayukan Al'umma da gidaje, kuma ya janyo Rashin aikin yi ga Al'umma. Ya bayyana cewa mutane basu kwanciyar hankalin da zasu tafiyar da rayuwarsu a tsinake, ko harkokinsu na yau da kullum.uma ya bayyana cewa Jama'a basu samun salloli Biyar a cikin Jam'i saboda fargabar abinda zai kasance,Saidai mutum yayi sallarsa a cikin gidansa saboda rashin samun nutsuwa. Dr.Ali Munguno ya kara da cewa yana rokonsu da su Amince a tattauna dasu domin a kawo karshen Asarar rayuka da ake. yace a matsayinsu na 'yan kasa suna da ikon rayuwa a jikin mutane ba tare da tsangwama ba. yace duka mu da su kasarmu ce, bamu da wata kasar da tafi wannan. kuma ya kara da cewa Gwamnatin tarayya tare da gwamnatin Jiha a hada hannu wajen tattaunawar domin a kawo karshen wannan Al'amari.

Wednesday, June 13, 2012

SARKIN YAKIN SARKIN MUSULMI DA GOBIRAWAN MADARUMFA

SARKIN YAKIN SARKIN MUSULMI!

 Kamar yadda kuka gani A sama Zamu kawo muku Tarihin Zuwan Sarkin Marma Muhammadu Madarumfa. Iyakar sokoto da Niger da kuma yakin da akayi tsakanin Muhammadu da Gobirawan Madarumfa, akan kogin da ya raba Niger da Nigeria, kusa da Jibya. A zamanin Sarkin Musulmi Abubakar Atiku Na Biyu Sarkin Hadejia Muhammadu yaje Sokoto dashi da mutanensa lokacin yana Sarkkn Marma, koda yaje sai ya iske ana yaki tsakanin rundunar Sarkin Musulmi da kuma Gobirawan Madarumfa. Yaki yayi tsanani gashi Dawakai da mutanen Sarkin Musulmi suna jin Kishi su kuwa Gobirawa sun tsare Ruwa,  Koda Sarkin Hadejia Muhammadu yaga haka sai ya nemi izni ga Sarkin Musulmi don a bashi dama dashi da mutanensa su shiga wannan yakin. Bayan an bashi izni sai yacewa Sakkwatawa yanzu zaku sha Ruwa koda jini ya gurbatashi, haka kuwa akayi Sarkin Hadejia da jama'a tasa suka shiga sukayi ta dauki ba dadi da Gobirawan Madarumfa har saida sukaci galaba a kansu, suka kore na korewa suka kashe na kashewa suka kama wasu a mazaunin Bayi. Bayan an gama yaki Sarkin Hadejia Muhammadu yazo yayi gaisuwa ga Sarkin Musulmi yace masa Ruwa ya samu aje asha a baiwa Dawakai. Bayan an koma Sokoto sai Sarkin Musulmi ya nada Sarkin Hadejia Muhammadu a matsayin Sarkin yakin Sarkin Musulmi saboda irin gudunmawa da ya bada. 

Bayan nadinsa a matsayin Sarkin yakin Sarkin Musulmi sai yayi Sallama da Sakkwatawa suka rakoshi har kan iyaka tare da jama'arsa suka kamo hanya suka dawo Hadejia. Kafin Sarkin Hadejia ya iso gida har labari ya samu Hadejiawa cewa an nada Muhammadu Sarkin yakin Daular Usmaniyya, dan haka sai jarumai da mahaya sukayi shjri sukazo suka taryeshi. 

A gaba zamu baku labarin shigowarsa Hadejia  da yadda aka kaiwa Sarkin Hadejia Haru Bubba Labarin Muhammadu. Harda Asalin Jafi da ake Ran sallah A kusa da Masallacin Juma'a. Muhammadu na Allah Ruwan kogi Tafi sannu sannu Wanda yayi wargi Ya Halaka. Giwa ta gama da Masu Karfi Ta wuce.

Monday, June 11, 2012

TARIHIN RAYUWAR MARIGAYI UMARU MUSA 'YAR-ADUA


Umaru Musa Yar'Adua
Shi dai marigayi Malam Umaru Babangida
Musa 'Yar'Adua, an haifeshi ne a ranar 16
ga watan Augustan 1951 a birnin Katsina
dake arewacin Najeriya. Mahaifinsa shine
tsohon ministan birnin Lagos na farko a
jamhuriya ta farko, kuma kafin ya rasu
shine Matawallen Katsina, sarautar da
kuma shi ma marigayi Umaru Musa
'Yar'Adua ya gada.

Marigayin ya fara makarantar Firamare ta
Rafukka a 1958 kafin a mayar da shi
makarantar Firamare ta kwana dake
Dutsen Ma a 1962. Ya kuma halarci
kwalejin gwamnati dake Keffi daga 1965
zuwa 1969. Sai kwalejin Barewa 1971,
inda ya samu takardar shedar karatu ta
HSC.
Tsohon shugaba 'Yar'Adua ya halarci
Jami'ar Ahmadu Bello dake Zariya daga
1972 zuwa 1978 inda ya samu takardar
shedar digiri akan kimiyyar haÉ—a sinadirai
ko Chemistry da Malanta, kafin ya koma
domin samun babban digiri duk dai akan
kimiyyar ta Chemistry.

Marigayin yayi bautar
ƙasa a jihar Lagos inda ya koyar a wata
makaranta da ake kira Holy Trinity daga
1975-1976.
Bayan da ya kammala aikin yiwa ƙasa
hidima ya fara aikin Malanta gadan-gadan
a kwalejin share fagen shiga jami'a da ake
kira CAST dake Zariya a tsakanin 1976
zuwa 1979.

A shekarar 1983 marigayi
Malam Umaru Musa 'Yar'adua ya bar aikin
Malanta ya fara aiki da Gonar Sambo Farms
a Funtua dake jihar Katsina inda ya zama
GM daga 1983-1989.
Daga shekarar 1984 bayan da Sojojin
sukayi juyin mulki malam Umaru Musa
'Yar'adua an kira shi domin zama wakili a
hukumar gudanarwar kanfanoni da
hukumomin gwamnati da dama da suka
haÉ—a da hukumar samar da kayan Noma
da kwalejin kimiyya da fasaha ta jihar
katsina, Bankin Habib da Hamada Carpets
da Madara Limited da kuma kanfanin buga
Jaridu da Mujalla ta The Nation wanda ke
kaduna kuma wansa Marigayi Janar Shehu
Musa 'Yar'Adua ya mallaka.


A lokacin da marigayi Malam Umaru Musa
'Yar'Adua ya shiga siyasa ya yi hannun riga
da mahaifinsa wanda a wancan lokaci yake
mataimakin shugaban Jam'iyar NPN, inda
shi kuma ya zama wakili a jam'iyar PRP ta
Malam Aminu Kano mai adawa da NPN. A
lokacin da Janar Babangida ya kaÉ—a gangar
siyasa ya zama sakataren jam'iyar SDP a
jihar ta Katsina kuma É—an takararta na
gwamna, amma kuma É—an takarar
jami'iyar NRC na wancan lokaci Malam
Saidu Barda ya kada shi.

To sai dai a 1999
Malam Umaru Musa 'Yar'Adua ya tsaya
takakarar muƙamin gwamnan jihar ta
Katsina kuma ya samu nasara a ƙarƙashin
jam'iyar PDP, haka kuma ya sake nasara a
zaɓen 2003.
A shekarar 2007 Umaru Musa 'Yar'Adua ya
zama ɗan takakar muƙamin shugaban
ƙasa na Jam'iyar PDP bayan ya samu
taimakon tsohon shugaban ƙasa Cif
Olusegun Obasanjo ya zama shugaban
ƙasa a ranar 29 ga watan Mayun 2007.
To sai dai rashin lafiya da tsohon shugaban
yayi fama da ita ta sanya bai samu sukunin
gudanar da harkokin mulki kamar yadda
yayi fata ba musanman ƙudirorinsa guda
bakwai daya tsara na ciyar da ƙasar gaba
kafin nan da ƙarni ta 2020.


Marigayi Malam Umaru Musa 'Yar'Adua ya
rasu a ranar 5 ga watan Mayun shekara ta
2010 da muke ciki a fadar gwamnati dake
Abuja watanni biyu bayan komowarsa gida
daga Saudiya inda yake jinya.
Ya kuma rasu ya bar mahaifiyarsa da
'yan'uwa da matar aure guda Hajiya Turai
tare da 'ya'ya bakwai da ya haifa da ita da
suka haÉ—a da mata biyar da maza biyu.
Haka kuma yana da wasu 'ya'ya biyu maza
da matarsa ta biyu Hajiya Hauwa Umar
Radda.

Thursday, June 7, 2012

ZUWAN TURAWA KASAR HADEJIA KASHI NA (2)


HADEJIA A YAU! A kashi na farko Na baku Labarin yadda Turawan mulkin mallaka suka yiwa Hadejia Leken Asiri, wadda hakan ta basu dama suka kama garin.

Yanzu zamu dora! Koda yake Sarkin Hadejia Muhammadu ya samu labarin Turawa sun ci Kano da Katagum duk sun koma karkashin mulkinsu yace da yabi Kafiri Gara yayi shahada,Turawa basu fasa ba shima bai fasa ba.

Ranar Talata 1906 Turawa suka shigo Hadejia Gadan gadan akayi ta gwabza fada, dukda dawakan Hadejia basu taba jin kukan Igwa ba da sunji wannan kukan sai su turje haka nan akayi ta fama da su. jama'ar Hadejia manya da yara kowa yayi shirin yaki haka nan akayi yaki har Zuwa Azahar,  kuma Turawa suna kara shigowa Hadejia, saboda makaman su ba irin namu bane. An kashe manyan fadawan Hadejia da hakimai:

kamar yadda na fada a baya Sarkin Hadejia Muhammadu saida aka ce masa Kada Hadejia ta kare saboda shi Tukuna ya rusuna har Turawa suka cim masa. Allahu akbar!

koda Hadejiawa suka samu labari an kashe sarki sai kowa ya Rusuna,  Turawa suka shigo Hadejia suka Fara shirin tafiyar da mulki irin nasu. Hadejiawa sukayi Jana'izar wadanda suka mutu, wadanda kuma sukaji rauni aka kaisu Gidajensu. Turawa suka Nada Sarkin Hadejia Haru mai karamba 1906. 

To akwai sarkin yaki cilin Yana daga cikin wadanda suka samu raunuka a yakin kuma shi Captai phillips ya sanshi dama can. to kullum sai yaje Gidan sarkin yaki Yana Masa Izgilanci yana ce masa ina yakin? Ashe Sarkin yaki yana jin ciwon hakan. Wata rana sai yacewa matarsa Idan zata Kawo masa Abinci tasa wuka a cikin Tuwon.

haka kuwa tayi. saida captain phillips yazo yana masa Izgili Sai yasa hannu kamar mai cin tuwo sai ya dauko wuka ya Burmawa captain phillips a tumbinsa ya kasheshi. Kabarinsa yana can a Gabas Da Bariki Hanyar Tandanu. Shi ake cewa Kabarin mai tumbi. Wadanda suka rasa rayukansu a yakin suna da dama Amma ga kadan daga Sunayensu. Muhammadu Sarkin Hadejia, Madacima shi suka fara kashewa, Galadima, Ma'aji salihu, Furya, Barwa da Tarno, Bori na Salihu, Kaura Amadu, Mabudi zakar, Jarma warkaci, Sabo jikan Tete, Dandalma, Abdulwahabu sarkin Baka, Sarkin Arewa, Alkali, Farau farau, Sarkin Dawaki Dan gazau, Da dai Sauransu! Allah yaji kansu da Rahma.

ZUWAN TURAWA KASAR HADEJIA 1906 (1)


HADEJIA A YAU! A shekarar 1906 Turawan mulkin mallaka suka ci Hadejia da yaki, Inda yayi sanadiyar mutuwar mutanen Hadejia da dama da kuma wasu daga cikin Turawan. kafin wannan Turawa sun shigo Hadejia ne bayan sun ci Katagum da yaki, koda yake ba yaki sukayi da Katagum ba, sun Meka musu wuya ne ba tare da jayayya ba.

kuma Turawan sun shigo Hadejia ne ta Iyakar kasar Hadejia da Katagum, Inda sukayi sansani a Mai Goriba kusa da Masama. To basu shigo Hadejia ba sai da suka turo Dan leken Asiri wadda ya shigo Hadejia a Matsayin Balarabe mai saida kayan Sarauta Irinsu Alkybba da sauransu. kuma an saukeshi a Gidan Zangoma Wato sarkin Baki.

kuma a haka yayi ta Kewaya Hadejia har ya gane duk sirrin Garin Haka kuma yana kaiwa Sarki kaya yana saye har yasan Sirrin fadar Hadejia.

Wannan dan leken Asirin da yayi shigar Balarabe shine Captain H. C. B. Phillips, Wadda ake ce masa (Mai Tumbi). Kuma kafin suzo Hadejia an basu labarin Garin da kuma Mayakan garin, dan haka shi Captain phillips ya dinga bin Gidajen Jarumai yana Musu alheri a Matsayinsa na dan kasuwa, hakan tasa ya shiga jikinsu sosai kuma suka Amince dashi.

Tuesday, May 29, 2012

NIGERIA

In 1979, Bamanga Tukur was the Governor of
the defunct Gongola State (now Adamawa &
Taraba) and 33 years after he is today the
Chairman of the ruling Party, The PDP; Dr. Bello
Halliru was commissioner in the Old Sokoto
State (now Sokoto, Kebbi & Zamfara) and 33
years after he is today Minister of Defence;
Major General David Mark (rtd) was the
military governor of Niger State in 1984 and
28 years after he is today the Senate
President; Gov. Murtala Nyako was the
governor of Niger State in 1976 and 36 years
after he is today the Governor of Adamawa
State; Ogbonnaya Onu was governor of Abia
State in 1992 and 20 years after he is today
the National Chairman of ANPP; Gov. David
Jonah Jang was the governor of Benue State
in 1985 and 27 years after he is today the
governor of plateau state; and Martins Elechi
the Ebonyi State Governor is over 80 years
old! Only in Nigeria is this possible, where the
youth of today have no hope into the future!

TRIBUTE TO SHEIKH JA'AFAR

TRIBUTE TO SHEIKH JA'AFAR MAHMOUD ADAM:
1) HIS EARLY CHILDHOOD : Late Sheikh Ja’afar
Mahmud Adam was born on February 12,
1960 in the ancient city of Daura in present
day Katsina State. He started learning his
Qur’anic education from Malam Haruna, the
husband of his elder sister. From there he
was taken to Fagge town in Kano in 1978,
where he began the memorization of the Holy
Qur’an under the guidance of Malam
Abdullahi.
His thirst for knowledge took him further to
an Arabic Institution which was under the
Egyptian Cultural Centre, situated at Bello
Dandago Road, Kano in 1981. He was, within
the same period, attending an Adult
Education School, situated at Shahuci. He
usually attended the Arabic Institution at
noon and the Adult Education School in the
evening.
In 1984, he was admitted into the
Government Teachers’ College, Gwale, Kano.
He graduated in 1988 and in 1989, he
secured admission into the prestigious
Islamic University in Madinah, Saudi Arabia,
where he studied for three years and
graduated in 1993. Some of the famous
scholars that taught Sheikh Ja’afar include
Sheikh Abdul Rafi’i, Dr. Mahmud Abdul Haliq
and Dr. Khald As-Sabat.
When he returned from Saudi Arabia, he got
admitted in the Bayero University, Kano. He
however could not finish the programme due
to some reasons. But nevertheless, he had his
second degree from the International
University of Africa in Sudan.
2) HIS TEACHING AND DA'AWA ACTIVITIES:
Teaching and Da'awah Activities
Upon his return from Madinah, Sheikh Ja’afar
set up the Usman Bin Affan Centre which
became autonomous in 1995. There, Shaikh
Ja'afar taught various subjects like Tafsirul
Qur’an (Qur’anic commentary) every Friday
between Maghrib and Isha prayers, Nahwu
on Saturdays between 8:00am and 9:30am,
Sirah on Sundays at the famous Almuntada
Mosque in Dorayi where he also leads Jumuah
prayers, and Tafsir at the Beirut Mosque, and
various other subjects at various schools and
institutions across the country.
He also conducted Tafsir annually in
Maiduguri during Ramadhan. He was also the
head of the Usman Bin Affan Islamic Trust. At
various times, he represented Nigeria
internationally in Qur’anic recitation
competitions where he emerged victorious
and did the nation proud. He is a member of
the "Ulama Consultative Forum" in Zamfara
and Bauchi states. He also presented various
Islamic programmes on radio and television
stations like Radio Kaduna, Bauchi Radio
Corporation, CTV Kano, DITV Kaduna, NTA
Borno, OITV Damaturu, and NTA Yola, among
others.
3) SHEIKH JA'AFAR SUDDEN DEPARTURE: On
Friday, 13th April 2007, at around 5:30am,
Shaikh Ja'afar fell to the bullets of suspected
hired assassins while leading the Subhi
prayer at the Dorayi Juma’at Mosque. The
assassins, numbering about five, shot Shaikh
Ja'afar at close range tearing his chest and
abdomen, as reported in the media. Soon
after the incident he was immediately rushed
to the Malam Aminu Kano Teaching Hospital
(AKTH) where he died before he could receive
medical attention.
It was also reported that the gunmen had
earlier stopped at his former mosque at
Gadon Kaya before they finally caught up with
him at the Dorayi mosque where he was
murdered.
Shaikh Ja'afar died at 45 and was survived by
three wives and five children. Truly, the
Ummah has lost a gem but the worst losers
are his killers. We pray to Allah (SWT) in His
Infinite Mercy to forgive Shaikh's sins, accepts
all his good deeds and grant him jannatul
firdaus, ameen.

Sunday, May 27, 2012

CHILDREN DAY BY DEMOLA ADEOYO

The Only GIFT Nigerian Adults Can Give
Nigerian Children For The May 27th Children's
Day Celebration Is
"Assurance Of A Better Country Starting
Today"
As We Were Given Back Then By Our Fathers
That Made Us Who We Are At A Point
Before We Allowed Greed To Overtake Our
Sense Of Responsibility.
Imagine If Our Fathers Were Like Us,
What Would Have Become Of Us Today?
No More Promises Of A Better Tomorrow.
No More!!!
HAPPY CHILDREN'S DAY Celebration To Our
Future Leaders.
May Your Time To Lead This Country
Never Be A Waste Like Your Parents Are Doing
Today.
God Bless U All And Make U Bring Back The Old
Glory Of Nigeria,
Which Your Fathers Have Frittered Away Like
The Prodigal Son
For An Empty Plate Of Porridge.

Friday, May 25, 2012

RANAR JUMA'A

Ranar jumaa itace mafi alherin dukkan wata
rana da rana ta fito a cikinta. cikinta Allah ya
halicci Adam, cikinta ne qiyama zata tsayu,
kuma ita ranar idi ice ga musulmai.Don haka
nema aka sharanta wasu abubuwa acikinta,
daga ciki akwai: hudubar jumaa, wanka,
fesa tirare, fita cikinta da mafi kyawun kaya
da yanayi me kyau, yin kabarbari lokacin fita
sallar, kusantar liman, da kuma tara tunani
gaba daya domin sauraren wa'azi da
ambato (wato huduba).